11
Sep
Daga JOHN D. WADA a Lafiya Kamar sauran jihohin ƙasar nan da ake sa ran gudanar da zaɓukan gwamnoni na shekarar 2023 dake tafe, a yanzu shirye-shirye da zirga-zirgar siyasa sun yi ƙamari a Jihar Nasarawa inda ‘yan takarar kujerar ta gwamnan jihar a duka jam’iyyu daban-daban ke cigaba da yin duka mai yuwa don tabbatar da sun yi nasarar lashe kujerar wadda a yanzu gwamnan jihar mai ci, Injiniya Abdullahi Sule na Jam’iyyar APC ne ke zaune a kai. Kamar dai yadda aka sani, Gwamna Abdullahi Sule wanda wa’adin mulkinsa zai qare ranar 29 ga watan Mayun shekarar 2023…
