Kasashen Waje

Harƙallar nukiliya: Iran ta ƙi amincewa ta tattauna da Amurka da Turai

Harƙallar nukiliya: Iran ta ƙi amincewa ta tattauna da Amurka da Turai

Daga AISHA ASAS Ƙasar Iran ta ce ba yanzu ne lokacin da ya dace a yi magana kan batun makaman nukiliya ba duba da halin da ƙasashen Amurka da Turai suka nuna. Iran ta ƙi amincewa da ta yi zaman tattaunawa da ƙashashen Amurka da Turai domin tattauna yadda za a farfaɗo da yarjejeniyar nukilya ta 2015, tana mai cewa dole sai Amurka ta ɗage duka takunkuman da ta ƙaƙaba mata kafin ta amince. A cewar mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Iran, Saeed Khatibzadeh, la'akari da halin da Amurka da wasu ƙasashen Turai suka nuna, ya sa Iran…
Read More
Myanmar: An yi arangama tsakanin magoya bayan sojoji da ɓangaren Suu Kyi

Myanmar: An yi arangama tsakanin magoya bayan sojoji da ɓangaren Suu Kyi

Rahotanni daga Ƙasar Myanmar sun nuna cewa, magoya bayan sojin da suka yi juyin mulki a ƙasar sun yi arangama da masu adawa da kifar da gwamnatin Aung San Suu Kyi a birnin Yangon, yayin da hukumomi suka daƙile ɗalibai a makarantunsu don hana su zanga-zanga. Tun lokacin da sojoji suka yi juyin mulki a ranar 1 ga Fabairu, tare da tsare Suu Kyi, ƙasar ta tsunduma cikin tashin hankali. Kimanin makonni uku kenan da ake gudanar da zanga-zanga a kowacce rana da kuma yajin aiki a ƙasar. Sai dai ‘yan sanda sun rufe ƙofofin makarantun da nufin hana ɗarruruwan…
Read More
Saudiyya: Zaki Yamani ya rasu

Saudiyya: Zaki Yamani ya rasu

Daga FATUHU MUSTAPHA Allah Ya yi wa fitaccen tsohon Ministan Harkokin Mai na Saudiyya, Ahmed Zaki Yamani, rasuwa. Yamani ya rasu ne a wata asibitin Landa a Litinin da ta gabata. Wata 'yar marigayin mai suna Mai Yamani, ta ce matsalar zuciya ce ta yi ajalin mahaifin nata, inda ya rasu yana da shekara 90. Yamani na ɗaya daga cikin mutanen da ƙasar Larabawa ba za ta mancewa da su ba saboda irin rawar da ya taka wajen cigabanta. A halin rayuwarsa, marigayin ya yi tsayin daka wajen bunƙasa harkokin mai na ƙasar Saudiyya. A matsayinsa na ministan albarkatun mai…
Read More
Bayan shekara 10, New Zealand na jimamin girgizar ƙasar da ta fuskanta

Bayan shekara 10, New Zealand na jimamin girgizar ƙasar da ta fuskanta

Daga WAKILIN MU A wannan Litinin ne Ƙasar New Zealand ke cika sheka 10 da faruwar ibtila'in girgizar ƙasa da ya auku a birnin Christchurch wanda ya yi sanadin mutuwar mutum 185, tare da jikkata wasu dubbai. Girgizar ƙasar wadda ta kai ƙarfin maki 6.3 da zurfin kilomita 5, ta faru ne a ranar 22, Fabrairu, 2011. Domin tuna zagayowar wannan rana, ɗaruruwan 'yan ƙasar ne suka taru a wani wajen taro a birnin Christchurch domin tunawa da duka waɗanda suka rasa rayukansu a wancan lokaci. Haka nan, an ga yadda aka yi ƙasa-ƙasa da tutoci a sassan ƙasar domin…
Read More
Korona ta yi ajalin mutum milyan biyu a faɗin duniya – Bincike

Korona ta yi ajalin mutum milyan biyu a faɗin duniya – Bincike

Daga WAKILIN MU A halin da ake ciki, adadin mutanen da cutar korona ta aika lahira a faɗin duniya ya kai milyan 2,441,917 kamar yadda sakamakon binciken Jami'ar Johns Hopkins ya nuna. Haka nan, jami'ar ta ce adadin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar a sassan duniya ya kai milyan 110.3. Sai dai, sakamakon binciken jami'ar ya nuna an samu raguwar adadin mutanen da kan kamu da cutar a cikin yini a faɗin duniya. Inda ya nuna a Talatar da ta gabata aka samu mafi ƙarancin adadi na waɗanda ke kamuwa da cutar a yini. A cewar jaridar Wall…
Read More
Cutar koron: Zimbabwe ta karɓi tallafin allurar rigakafi daga Chaina

Cutar koron: Zimbabwe ta karɓi tallafin allurar rigakafi daga Chaina

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga ƙasar Zimbabwe sun nuna jirgin saman da ke ɗauke da allurar rigakafin annobar cutar korona wadda ƙasar Sin ta bayar gudunmawa ga ƙasar ya isa filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na Robert Mugabe da ke Harare, babban birnin kasar, da asubahin wannan Litinin. Da yake jawabi a filin jirgin, Mataimakin Shugaban Ƙasar Zimbabwe Constantino Chiwenga, ya ce ƙasar Sin ta jima tana taimaka wa Zimbabwe kan sha'anin yaƙi da annobar korona, kuma gudunmawar rigakafin zai taimaka wa ƙasar a yaƙin da take yi da annobar. Kazalika, Chiwenga ya ce gudunmawar za ta yi tasiri…
Read More
Afirka ta Kudu ta fasa shirin yi wa ‘yan ƙasar rigakafin korona

Afirka ta Kudu ta fasa shirin yi wa ‘yan ƙasar rigakafin korona

Daga AISHA ASAS Ƙasar Afirka ta Kudu ta ce ta fasa shirin yi wa 'yan ƙasar allurar rigakafin cutar korona da ta so somawa bayan da ta gano cewa gwajin maganin AstraZeneca jab da ta yi ya kasa yaƙar nau'in cutar da ya bayyana a ƙasar. Afirka ta Kudu ita ce ƙasar da ta fi kowace ƙasa harbuwa da cutar a faɗin nahiyar Afirka, inda ta so soma aiwatar da shirin yi wa 'yan ƙasar allurar rigakafin korona da ta mallaka daga AstraZeneca da Oxford. A cewar Ministan Lafiyar ƙasar Zweli Mkhize, "Mun dakatar da rigakafin na wucin-gadi har sai…
Read More
Cutar Korona: Abu Dhabi ta haramta tarurrukan shaƙatawa da na bukukuwa

Cutar Korona: Abu Dhabi ta haramta tarurrukan shaƙatawa da na bukukuwa

Daga BASHIR ISAH A matsayin wani mataki na yaƙi da yaɗuwar annobar korona a Abu Dhabi, Kwamitin Kula da Agajin Gaggawa, rikice-rikice da Ibtila'i na Abu Dhabi ya sanya dokar haramta tarurrukan shaƙawata da na bukukuwa a faɗin birnin sai dai ɗan abin da ba za a rasa ba. Kwamitin ya ce daga ranar 7 ga Fabrairun 2021, an taƙaita adadin mutane da aka amince su halarci taron bikin aure da na zumunta zuwa mutum 10, sannan mutum 20 game da tarurrukan da suka shafi jana'iza da zaman makoke. Haka nan an taƙaita yawan mutanen da aka yarda su gudanar…
Read More
Myanmar: An maka Suu Kyi a kotu

Myanmar: An maka Suu Kyi a kotu

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga ƙasar Myanmar sun tabbatar da cewa an gurfanar da jagorar Myanmar, Aung San Suu Kyi gaban kotu a Larabar da t gabata, kwanaki biyu bayan tsare ta da sojojin da suka kifar da gwamnatin ƙasar suka yi. Kazalika, bayanai sun ce, kiraye-kirayen tada ƙayar baya don nuna adawa da juyin mulkin ƙasar sai ƙaruwa suke. Ƙasar Myanmar da ke Kudu maso gabashin nahiyar Asiya ta sake faɗawa cikin mulkin soji ne bayan da wasu gungun sojoji suka damƙe jagororin mulkin farar hula a Litinin da ta gabata, lamarin da ya kawo ƙarshen mulkin dimokraɗiyyar ƙasar…
Read More
Myanmar: Magoya baya sun buƙaci a sako Suu Kyi da sauransu

Myanmar: Magoya baya sun buƙaci a sako Suu Kyi da sauransu

Daga WAKILIN MU 'Yan jam'iyyar National League for Democracy a ƙasar Myanmar, sun yi kira da a sako Aung San Suu Kyi tare da sauran jagororinsu da aka tsare a Talatar da ta gabata. Suna masu bayyana juyin mulkin da sojojin ƙasar suka yi a ƙasar a matsayin al'amari da ya yi wa tarihin sojin ƙasar tabo mara kyau. Da sanyin safiyar Litinin da ta gabata sojoji suka kama Suu Kyi da ta kasance shugabar jam'iyyarsu tare da shugaban ƙasar, Win Myint. Bayan juyin mulkin, ba tare da ɓata lokaci ba sojojin suka naɗa wani tsohon janar, Min Aung Hlaing,…
Read More