17
Mar
Daga JOHN D. WADA a Lafiya Ɗan takarar kujerar Gwamnan Jihar Nasarawa a inuwar Jam’iyyar NNPP, Alhaji Yakubu Maidoya ya ƙaryata jita-jitar da wasu a jihar ke yaɗawa a yanzu cewa ya janye wa gwamnan jihar wanda shine kuma ɗan takarar Jam’iyyar APC mai ci a jihar, Injiniya Abdullahi Sule. Alhaji Yakubu Maidoya ya sanar da haka ne a jawabinsa a lokacin wata tattaunawar haɗin gwiwa da jam’iyyarsa ta NNPP da ‘yan takarar gwamnan a inuwar jam’iyyun SDP da ADC wadda suka gudanar da manema labarai a babbar sakatariyar ‘yan jarida dake Lafiya, babban birnin jihar ranar Laraba 15 ga…
