18
Mar
Daga UMAR GARBA a Katsina Ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a ƙarƙashin jam'iyyar APC, Dr. Dikko Umar Raɗɗa, ya ce yana da yaƙinin shi ne zai lashe zaɓen jihar. Raɗɗa ya bayyana haka ne ranar Asabar jim kaɗan bayan da shi da mai ɗakinsa, Hajiya Zulaihat suka kaɗa ƙuri'arsu a mazaɓar Katuka mai lamba 010 da ke mahaifar ɗan takarar dake Ƙaramar Hukumar Charanci ta jihar Katsina. A zantawar da ya yi da manema labarai, Raɗɗa ya ce, "Na zo don kaɗa ƙuri'ata a matsayin haƙƙin ɗan ƙasa. "Ina fata zaɓen zai samar wa al'umar Jihar Katsina shugaba nagari, don…
