Wasanni

Kenya: An yanke wa ‘yar wasan tsere hukuncin shekara guda saboda amfani da maganin ƙara kuzari

Kenya: An yanke wa ‘yar wasan tsere hukuncin shekara guda saboda amfani da maganin ƙara kuzari

Daga FATUHU MUSTAPHA Wata kotun ƙasar Kenya ta yanke wa ‘yar wasan tseren asar, Florence Jepkosgei, hukuncin yi wa al’umma hidima na tsawon shekara guda bayan da ta kama ta da laifin gabatar da takardun bogi na ƙoƙarin kare kanta daga laifin yin amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari, in ji Ƙungiyar Yaƙi da Amfani da Abubuwan Ƙara Kuazara ga ‘Yanwasa ta Kenya (ADAK). Da wannan, Florence ta zama ‘yar tseren Kenya ta farko da aka taɓa yanke wa hukuncin manyan laifuka a kotu. An shafe shekaru ana gudanar da bincike kan wannan batu kafin a kai ga yanke hukunci a…
Read More
’Yan wasan damben boksin da su ka fi samun kuxi a duniya

’Yan wasan damben boksin da su ka fi samun kuxi a duniya

Daga UMAR M. GOMBE Ɗaya daga cikin manyan wasannin da suka fi shahara a duniya shi ne, wasan damben zamani da ake kira a turance da Boxing. Kusan a iya cewa wannan wasa na cikin wasanni mafiya daɗewa a duniya, domin kuwa wasan dambe wasa ne da kusan ba wata al’umma da bata yi. Masana sun gano cewa, akwai shaidu na tarihi da suka nuna shekaru 3000 kafin bayyanar Annabi Isa ana wannan wasa a tsohuwar Daular Misra. Amma wasan ya fara samun tagomashi ne a ƙarni na 7 tunda aka fara yin sa a wasan Olympic. Sai dai duk…
Read More
Gasar ƙwallon ƙafa: Ekiti ta shirya karɓar baƙi

Gasar ƙwallon ƙafa: Ekiti ta shirya karɓar baƙi

Daga BASHIR ISAH A halin da ake ciki jihar Ekiti ta ce ta shirya tsab domin karɓar baƙuncin ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa su 16 daga jihar Kwara da na sauran jihohi daga shiyyar Kudu maso-yamma sakamakon gasar ƙwallon ƙafa ta ƙasa da aka shirya gudanarwa a jihar. A zantawarsu da manema labarai, Shugaban Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa na Jihar, Ekiti Bayo Olanlege, ya bayyana farin cikinsa tare da bada tabbacin cewa jihar ta shirya karɓar baƙi albarkacin gasar. Olanlege ya yi amfani da wannan dama wajen yi wa baƙinsu albishir da cewa lallai za su ji daɗin gwargwadon zaman da za su…
Read More
Minista Dare ya ƙaddamar da gasar ‘Principal Cup’

Minista Dare ya ƙaddamar da gasar ‘Principal Cup’

Daga BASHIR ISAH An ƙaddamar da gasar ƙwallon ƙafa na 'Principal Cup'. Ministan Matasa da Wasannin Motsa Jiki, Mr Sunday Dare ne ya ƙaddamar da gasar a birnin Legas a wannan Juma'a. Bayan ƙaddamar da gasar, Igbobi da kuma Government College Kaduna, su ne suka fara fafatawa a filin wasannin motsa mitsa jiki na Agege, Legas. A cewar Minista Dare wanda shi ne silar farfaɗo da gasar 'Principal Cup', " Cikar buri ne kuma abin farin ciki ganin wannan gasa ta kankama a yau. "Muna alfahari da wasan da waɗannan matasa suka yi a yau. Ina fata wannan zai zama…
Read More
FIAN ta nuna takaicinta kan yadda ƙungiyoyi kan gaza kula da ‘yanwasa

FIAN ta nuna takaicinta kan yadda ƙungiyoyi kan gaza kula da ‘yanwasa

Ƙungiyar Masu Shiga-tskanin Harkokin Ƙwallon Kafa ta Kasa (FIAN), ta nuna damuwarta kan yadda masu ruwa da tsaki kan harkokin ƙwallon ƙafa ba su ɗaukar lamarin 'yan ƙwallon da muhimmanci wajen biyan albashinsu da alawus-alawus da makamantansu yadda ya dace. Shugaban FIAN na ƙasa, Ayodele Thomas, ya nuna damuwarsa kan yadda masu ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa suke nuna halin ko-in-kula wajen kula da sha'anin 'yan wasansu yadda ya kamata. Da yake zantawa da manema labarai, Thomas ya ce abin takaici ne yadda masu kulob-kulob kan gaza wajen lura da 'yan ƙwallonsu bilhaƙki. Ya ce kamata ya yi kafin ƙungiya ta ɗauki…
Read More
An sako direban Adamawa United da aka yi garkuwa da shi

An sako direban Adamawa United da aka yi garkuwa da shi

Daga WAKILIN MU An sako direban Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa na Adamawa United wanda aka yi garkuwa da shi a ranar Asabar da ta gabata. An yi garkuwa da direban ƙungiyar ne a lokacin da suka faɗa hannun wasu 'yan fashi da makami a kan hanyarsu ta zuwa birnin Legas don buga wasan da aka tsara musu a can. Yazu haɗa wannan labari, babu wani cikakken bayani a kan ko sai da aka biya diyya kafin aka saki direban. Tun farko, 'yan fashin sun buƙaci a biya diyyar naira milyan N50 kafin su saki direban da suka yi garkuwa da shi,…
Read More
‘Yan fashi sun cika wa ‘yan ƙungiyar Adamawa United aiki

‘Yan fashi sun cika wa ‘yan ƙungiyar Adamawa United aiki

Daga FATUHU MUSTAPHA 'Yan ƙungiyar ƙwallon ƙafa na jihar Adamawa, wato Adama United, sun gamu da wasu 'yan fashi a hanyar Benin zuwa Ore a Juma'ar da ta gabata. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna 'yan fashin sun ƙwace wa 'yan wasan da jami'an ƙungiyar wasu kayayyakinsu haɗa da kuɗaɗe. 'Yan wasan suna kan hanyarsu ta zuwa Legas ne domin buga wasan da aka tsara za su buga tare da ƙungiyar MFM a nan Legas inda suka gamu da 'yan fashin da misalin ƙarfe 11:45pm. Wannan dai shi ne karo na uku da ake samu wata babbar ƙungiyoyin ƙwallon…
Read More
Yadda wasan damben gargajiya ke karɓuwa a Nijeriya

Yadda wasan damben gargajiya ke karɓuwa a Nijeriya

Daga FATUHU MUSTAPHA Wasan damben gargajiya baya buƙatar wani dogon gabatarwa ga masu karatu, domin wasa ne da ya shahara ba ma a nan ƙasar ba, har ma faɗin Afrika ta Yamma gaba ɗaya. Hausawa dai kan masa kirari da “Saga wasan mahaukata, mai hankali yana na daina mahaukaci yana zan fara.” Ba muda wani cikakken bayani akan lokacin da aka fara wasan damben a tarihin Ƙasar Hausa, sai dai shaidu na tarihi sun nuna irin tasirin sa a rayuwar Bahaushe tun shekaru aru aru da suka shuɗe. Babban misali na daɗewar wasan dambe shi ne abinda muka samu daga…
Read More
Wasan dambe: Usman ya lashe  kambun UFC karo na uku

Wasan dambe: Usman ya lashe kambun UFC karo na uku

Daga WAKILIN MU Dan wasan damben nan Kamaru Usman, wanda ɗan asalin Nijeriya ne, ya sake lashe kambunsa na UFC bayan da ya doke Gilbert Burns daga ƙasar Brazil a karawar da suka yi a Lahadin da ta gabata. Wannan shi ne karo na uku da Usman ke samun nasarar lashe wannan kambu. Ya samu nasarar farko ne a 2019 bayan da ya doke Colby Covington, sai ta biyu da ya samu a 2020 bayan da ya doke Jorge Masvidal. Yayin wasan baya-bayan nan, Usman bai yi wa Burns da wasa ba inda ya bambance masa tsakanin aya da tsakuwa.…
Read More
Tsohon ɗanwasan Super Eagles ya rasu

Tsohon ɗanwasan Super Eagles ya rasu

Daga WAKILIN MU Tsohon ɗan wasan Super Eagles Yisa Sofoluwe, ya rasu. Sofoluwe ya rasu ne a Talatar da ta gabata a Asibitin Koyarwa ta Jami'ar Legas bayan fama da ya yi da lalurar ƙwaƙwalwa. Tun farko sai da aka kai marigayin wata asibiti a yankin Ikorodu kafin daga bisani aka ɗauke shi zuwa asibitin jami'ar Legas. A halin rayuwarsa, marigayin ya buga wa Nijeriya wasa da dama, ciki har da gasar cin kofin Afirka (AFCON) a 1984 da 1988. Haka nan, ya samu zarafin buga ma wasu manyan ƙungiyon ƙwallon ƙafa na ƙasa, irin su 3SC da Julius Berger…
Read More