Wasanni

Manchester United ta fara tattaunawa da Ruben Amorim bayan ta kori Erik ten Hag

Manchester United ta fara tattaunawa da Ruben Amorim bayan ta kori Erik ten Hag

Kocin Sporting Lisbon, Ruben Amorim, ya amince da zama sabon kocin Manchester United bayan tsige Erik ten Hag a ranar Litinin, a cewar TalkSport. Manchester United sun fara tattaunawa da ɗan shekara 39 ɗin game da wannan muƙamin, inda ƙungiyar ta shirya biyan kuɗin sakin kwantiraginsa na €10m. Amorim yana da sha'awar karɓar aikin, kuma Manchester United za ta yi ƙoƙarin tattaunawa da Sporting Lisbon kan sauyawar kocin zuwa Ingila. Bayan korar ten Hag, sunan Amorim ya kasance daga cikin waɗanda aka tattauna da su don maye gurbinsa. Sauran waɗanda aka yi la’akari da su sun hada da tsohon kocin…
Read More
Yadda Liverpool ke nuna bajinta a ƙarƙashin Slot

Yadda Liverpool ke nuna bajinta a ƙarƙashin Slot

Liverpool ta cigaba da nuna bajinta a wannan kaka a ƙarƙashin kocinta Arne Slot, abin da ya sa ta ke ta kafa jerin tarihi a halin da ake ciki, kuma nasarta ta daren ya ci gaba da nuna yadda ta shiga wannan kaka da ƙafar dama. Liverpool ta doke RB Leipzig da ci ɗaya mai ban haushi a daren Laraba, a wasan zakarun nahiyar Turai. Leipzig na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da tsohon kocin Liverpool, Jurgen Klopp, wanda ya bar ƙungiyar bayan shafe shekaru 9 zai riƙa kulawa da su a matsayinsa na jagoran abin da ya shafi ƙwallon ƙafar…
Read More
 Vinicius ya cancaci lashe Ballon d’Or a bana – Ancelotti

 Vinicius ya cancaci lashe Ballon d’Or a bana – Ancelotti

Kocin Real Madrid Carlo Ancelotti ya ce Vinicius Jr zai lashe kyautar Ballon d'Or ta bana da za a yi a ranar 28 ga wannan watan na Oktoba. Vinicius ya ci wa Madrid ƙwallo uku a wasan da ta yi a jiya da Borussia Dortmund, wanda aka fara zura musu ƙwallo biyu a minti 45 ɗin farko. Bayan dawowa hutun rabin lokaci ne Madrid ta farke ta ci ƙwallo 5-2, kuma da tasirin Vinicius. "Zai lashe kyautar, ba wai don ƙwallayen da ya ci ba a daren jiya, saboda abin da ya yi a bara. "A bara ya taimaka mana…
Read More
Yadda Argentina ta lallasa Bolivia

Yadda Argentina ta lallasa Bolivia

Lionel Messi ya ci ƙwallo uku a wasan neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a 2026, wanda Argentina ta doke Bolivia 6-0. Wannan ne karo na 10 da Messi ke ci wa Argentina kwallo uku a wasa guda a tarihi. Dan wasan gaban Iter Miami mai shekara 37, wanda ya bayar da ƙwallo biyu aka ci a filin wasan na Monumental da ke birnin Buenos Aires, ya kamo takwaransa na Portugal Cristiano Ronaldo a yawan ƙwallo uku a ƙasarsu. Argentina da ke saman teburi ta bai wa Colombia maki uku a wasannin neman gurbin gasar kofin duniya…
Read More
Tuchel ya zama sabon kocin Ingila

Tuchel ya zama sabon kocin Ingila

An naɗa Thomas Tuchel a matsayin sabon kocin Ingila. Kwantiraginsa za ta fara ne daga 1 ga watan Janairun 2025. Dan ƙasar Jamus mai shekara 51, ya zama mutum na uku da zai jagoranci Ingila wanda ba ɗan ƙasar ba, bayan Sɓen-Goran Eriksson da Fabio Capello. Gareth Southgate ya yi murabus a watan Yuli bayan shan kashi da Ingila ta yi a hannun Sifaniya a wasan ƙarshe na Gasar Euro 2024. Lee Carsley, wanda aka naɗa a matsayin kocin riƙon ƙwarya a watan Agusta, zai ci gaba da riƙo a wasannin Gasar Nations League da Ingila za ta yi da…
Read More
AFCON: Nijeriya da Libya za su san matsayar su 22 ga watan Oktoba 2024

AFCON: Nijeriya da Libya za su san matsayar su 22 ga watan Oktoba 2024

Hukuncin da hukumar ƙwallon ƙafa ta Afrika (CAF) za ta yanke kan wasan neman cancantar shiga gasar AFCON na 2025 tsakanin Super Eagles da Libya da aka shirya yi a Benina, mai yiyuwa ne a sanar da shi ranar Talata, 22 ga Oktoba, 2024. CAF, wadda ta miƙa lamarin zuwa ga sashin ladabtarwa, za ta gana a Addis Ababa, Habasha, ranar Talata. Libya ta yi shirin karɓar baƙuncin Super Eagles da yammacin Talata a Benina, kusa da Benghazi, bayan da suka fara fafatawa da juna a Uyo a ci gaba da gasar neman cancantar shiga gasar AFCON ta 2023. Sai…
Read More
NPFL: Rivers United ta sake hawa saman tebur

NPFL: Rivers United ta sake hawa saman tebur

Rivers United sun ci gaba da samun nasara s a gasar Firimiyan Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NPFL) bayan sun doke Shooting Stars da ci 2-0 a Fatakwal, yayin da waɗanda ke saman teburin gasar Remo Stars suka sha kashi hannun Plateau United da ci 3-1 a Jos. Rivers United, ƙarƙashin jagorancin tsohon kocin Super Eagles Finidi George, yanzu suna da maki 17 daga wasa bakwai, yayin da Remo Stars suka sauka daga matsayi na farko tare da maki 15. Rivers United sun jira zuwa rabin lokaci na biyu kafin su zura ƙwallo ta hannun Aniekeme Okon a minti na 51.…
Read More
Yanzu-yanzu: Jirgin Super Eagles ya sauka a Nijeriya bayan wahalar da suka sha a Libya

Yanzu-yanzu: Jirgin Super Eagles ya sauka a Nijeriya bayan wahalar da suka sha a Libya

Daga USMAN KAROFI Tawagar Super Eagles sun iso Nijeriya bayan wahalar da suka sha a Libiya domin buga wasan cancantar shiga gasar cin Kofin Nahiyar Afrika ta 2025 (AFCON). 'Yan wasa da jami’an tawagar sun maƙale a filin jirgin sama na Libiya har tsawon sa’o’i 13 kafin wasan da aka shirya za a buga ranar Talata. Hotunan tawagar suna barci a kan kujerun filin jirgin sun bazu sosai a safiyar Litinin, wanda ya jawo suka daga 'yan Nijeriya da dama. Amma sa’o’i kaɗan bayan haka, tawagar ta sauka a Nijeriya bayan hukumomin Libiya sun ba da izinin jirginsu ya tashi.
Read More
Jami’an ƙasar Libya sun karkatar da jirgin ‘yan wasan Super Eagles  zuwa Al Abaq

Jami’an ƙasar Libya sun karkatar da jirgin ‘yan wasan Super Eagles zuwa Al Abaq

Rahotannin da ke zuwa na nuni da cewa a halin yanzu hukumomin ƙasar Libya na tsare da tawagar Super Eagles na Nijeriya a filin jirgin saman Al Abaq da ke birnin Al Abaq. Hakan ya biyo bayan karkatar da jirgin tawagar ne, mintuna kaɗan bayan ya sauka a Benghazi, inda nan ne dama zai sauka tun farko daga Abuja. Super Eagles tare da wasu ‘yan ƙasashen waje da ke gudanar da ayyukansu a Turai a halin yanzu suna maƙale a filin tashi da saukar jiragen sama, kamar yadda wani faifan bidiyo da hukumar ƙwallon ƙafar Nijeriya NFF ta fitar. Yanzu…
Read More
Man city ta doka wasanni 30 a jere cikin nasara

Man city ta doka wasanni 30 a jere cikin nasara

Kungiyar Manchester City ta yi nasara a kan Fulham 3-2 ranar Asabar a wasan mako na bakwai a firimiya a Etihad. Wasa na 30 kenan a Premier League a jere ba a doke City ba, tun bayan nasarar da Aston ɓilla ta yi a kanta a cikin Disambar 2023. Hakan ya sa ta yi kan-kan-kan da irin wannan bajintar da City ta yi tsakanin Afirilun 2017 zuwa Janairun 2018. Man City na fatan kafa sabon tarihin wasa 31 a jere ba tare da rashin nasara ba a ranar 20 ga watan Oktoba a wasa da Wolɓerhampton a Firimiya League. Arsenal…
Read More