Wasanni

Tuchel ya zama sabon kocin Ingila

Tuchel ya zama sabon kocin Ingila

An naɗa Thomas Tuchel a matsayin sabon kocin Ingila. Kwantiraginsa za ta fara ne daga 1 ga watan Janairun 2025. Dan ƙasar Jamus mai shekara 51, ya zama mutum na uku da zai jagoranci Ingila wanda ba ɗan ƙasar ba, bayan Sɓen-Goran Eriksson da Fabio Capello. Gareth Southgate ya yi murabus a watan Yuli bayan shan kashi da Ingila ta yi a hannun Sifaniya a wasan ƙarshe na Gasar Euro 2024. Lee Carsley, wanda aka naɗa a matsayin kocin riƙon ƙwarya a watan Agusta, zai ci gaba da riƙo a wasannin Gasar Nations League da Ingila za ta yi da…
Read More
AFCON: Nijeriya da Libya za su san matsayar su 22 ga watan Oktoba 2024

AFCON: Nijeriya da Libya za su san matsayar su 22 ga watan Oktoba 2024

Hukuncin da hukumar ƙwallon ƙafa ta Afrika (CAF) za ta yanke kan wasan neman cancantar shiga gasar AFCON na 2025 tsakanin Super Eagles da Libya da aka shirya yi a Benina, mai yiyuwa ne a sanar da shi ranar Talata, 22 ga Oktoba, 2024. CAF, wadda ta miƙa lamarin zuwa ga sashin ladabtarwa, za ta gana a Addis Ababa, Habasha, ranar Talata. Libya ta yi shirin karɓar baƙuncin Super Eagles da yammacin Talata a Benina, kusa da Benghazi, bayan da suka fara fafatawa da juna a Uyo a ci gaba da gasar neman cancantar shiga gasar AFCON ta 2023. Sai…
Read More
NPFL: Rivers United ta sake hawa saman tebur

NPFL: Rivers United ta sake hawa saman tebur

Rivers United sun ci gaba da samun nasara s a gasar Firimiyan Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NPFL) bayan sun doke Shooting Stars da ci 2-0 a Fatakwal, yayin da waɗanda ke saman teburin gasar Remo Stars suka sha kashi hannun Plateau United da ci 3-1 a Jos. Rivers United, ƙarƙashin jagorancin tsohon kocin Super Eagles Finidi George, yanzu suna da maki 17 daga wasa bakwai, yayin da Remo Stars suka sauka daga matsayi na farko tare da maki 15. Rivers United sun jira zuwa rabin lokaci na biyu kafin su zura ƙwallo ta hannun Aniekeme Okon a minti na 51.…
Read More
Yanzu-yanzu: Jirgin Super Eagles ya sauka a Nijeriya bayan wahalar da suka sha a Libya

Yanzu-yanzu: Jirgin Super Eagles ya sauka a Nijeriya bayan wahalar da suka sha a Libya

Daga USMAN KAROFI Tawagar Super Eagles sun iso Nijeriya bayan wahalar da suka sha a Libiya domin buga wasan cancantar shiga gasar cin Kofin Nahiyar Afrika ta 2025 (AFCON). 'Yan wasa da jami’an tawagar sun maƙale a filin jirgin sama na Libiya har tsawon sa’o’i 13 kafin wasan da aka shirya za a buga ranar Talata. Hotunan tawagar suna barci a kan kujerun filin jirgin sun bazu sosai a safiyar Litinin, wanda ya jawo suka daga 'yan Nijeriya da dama. Amma sa’o’i kaɗan bayan haka, tawagar ta sauka a Nijeriya bayan hukumomin Libiya sun ba da izinin jirginsu ya tashi.
Read More
Jami’an ƙasar Libya sun karkatar da jirgin ‘yan wasan Super Eagles  zuwa Al Abaq

Jami’an ƙasar Libya sun karkatar da jirgin ‘yan wasan Super Eagles zuwa Al Abaq

Rahotannin da ke zuwa na nuni da cewa a halin yanzu hukumomin ƙasar Libya na tsare da tawagar Super Eagles na Nijeriya a filin jirgin saman Al Abaq da ke birnin Al Abaq. Hakan ya biyo bayan karkatar da jirgin tawagar ne, mintuna kaɗan bayan ya sauka a Benghazi, inda nan ne dama zai sauka tun farko daga Abuja. Super Eagles tare da wasu ‘yan ƙasashen waje da ke gudanar da ayyukansu a Turai a halin yanzu suna maƙale a filin tashi da saukar jiragen sama, kamar yadda wani faifan bidiyo da hukumar ƙwallon ƙafar Nijeriya NFF ta fitar. Yanzu…
Read More
Man city ta doka wasanni 30 a jere cikin nasara

Man city ta doka wasanni 30 a jere cikin nasara

Kungiyar Manchester City ta yi nasara a kan Fulham 3-2 ranar Asabar a wasan mako na bakwai a firimiya a Etihad. Wasa na 30 kenan a Premier League a jere ba a doke City ba, tun bayan nasarar da Aston ɓilla ta yi a kanta a cikin Disambar 2023. Hakan ya sa ta yi kan-kan-kan da irin wannan bajintar da City ta yi tsakanin Afirilun 2017 zuwa Janairun 2018. Man City na fatan kafa sabon tarihin wasa 31 a jere ba tare da rashin nasara ba a ranar 20 ga watan Oktoba a wasa da Wolɓerhampton a Firimiya League. Arsenal…
Read More
Haaland ya shiga cikin gwarazan gasar firimiya na Satumba

Haaland ya shiga cikin gwarazan gasar firimiya na Satumba

Erling Haaland yana cikin 'yan takarar gwarzon gasar firimiya na watan Satumba, bayan da aka buga wasan mako na bakwai a karshe mako. Dan wasan City yana takara ne tare da Cole Palmer na Chelsea da Luis Diaz na Liverpool da Ollie Watkins na Aston villa da David Raya da Gabriel dukkansu daga Arsenal. Haalan mai shekara 24 ya taka rawar gani a watan Satumba, wanda ya zura ƙwallo uku a raga a wasa uku a firimiya. Ya fara da cin biyu a karawar da City ta doke Brentford 2-1 a Etihad, inda Pep Guardiola ya haɗa maki uku a…
Read More
Iniesta ya yi ritaya daga buga ƙwallon ƙafa

Iniesta ya yi ritaya daga buga ƙwallon ƙafa

Andres Iniesta ya sanar da yin ritaya daga buga wasa, mai shekara 40 da haihuwa. Wanda ya taɓa lashe kofin duniya da tawagar Sifaniya, ana cewa ɗaya ne daga cikin waɗanda suka yi fice a fannin tamaula a duniya a tarihi. Ya taka rawar gani a wasa da yake buga wa daga tsakiya a tawagar Sifaniya da ya yi da ɗaɓi Hernandez da Sergio Busƙuets da kuma a Barcelona. Ya buga wa Sifaniya wasa 131 da cin ƙwallon da ƙasar ta lashe kofin duniya a 2010 da ɗaukar kofin nahiyar Turai Euro a 2008 da kuma a 2012. Iniesta ya…
Read More
’Yan Nijeriya sun yaba wa Ahmad Musa da Shehu Abdullahi kan komawa Kano Pillars

’Yan Nijeriya sun yaba wa Ahmad Musa da Shehu Abdullahi kan komawa Kano Pillars

’Yan Nijeriya, musamman ’yan arewa sun yaba wa matakin tsohon Kaftin ɗin tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya Ahmed Musa tare da Shehu Abdullahi, shi ma tsohon ɗan wasan na Super Eagles, na komawa buga wasa a Kano Pillars. Karo na uku kenan da Ahmad Musa ke haskawa a gasar Firimiyar Nijeriya, inda a wasansa na farko da ya bugawa Pillars inda ya jefa duka ƙwallaye biyun da suka doke Sunshine Stars da su a karawar da suka yi a ranar Lahadi. Wannan nasara da  Pillars ta samu, ta sanya ta kai wa matsayi na 7 da maki 7. Ahmed Musa da…
Read More
Raya ya zama gwarzon ɗan wasan Arsenal na Satumba

Raya ya zama gwarzon ɗan wasan Arsenal na Satumba

David Raya ne ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan Arsenal na watan Satumba, wanda magoya bayan ƙungiyar suka zaɓa. Wanda ya lashe safar zinare a matakin wanda ƙwallaye da yawa bai shiga ragarsa ba da a bara, karon farko da ya zama gwarzon Gunners na wata. A labarin da Arsenal ta wallafa a shafinta na Intanet, Raya ya doke wadanda suka yi takara da ya haɗa da Gabriel da Bukayo Saka da William Saliba ka ƙuri'a kaso 44 cikin 100. Ya buga wasan Tottenham ƙwallo bai shiga ragarsa ba da taka rawar gani a Atlanta da tare penaritin Mateo Retegui,…
Read More