09
Nov
Alamu masu ƙarfi na nuna cewa Man City ta fara kakar wasan bana da ƙafar hagu, inda kocinta, Pep Guardiola ya ce abubuwa na ƙara yin tsauri a wasannin da suke dokawa. Ranar Asabar, Man City mai riƙe da kofin firimiyar Ingila ta yi rashin nasara 2-1 a gidan Bournemouth, kafin nan aka yi waje da ita a Carabao Cup a hannun Tottenham 2-1, sannan a daren Talata kuma ta sha kashi hannun Sporting a gasar Zakarun Turai. Karon farko da aka ci Man City a firimiya, wadda ta yi wasa 32 a jere ba tare da an doke ta…
