Wasanni

Pique zai yi ritaya daga buga wasan ƙwallon ƙafa gobe

Pique zai yi ritaya daga buga wasan ƙwallon ƙafa gobe

Daga NASIR S. GWANGWAZO Ɗan wasan baya na Ƙungiyar Barcelona, Gerard Pique, ya bayyana shirinsa na yin ritaya daga wasan ƙwallon ƙafa bakiɗaya a gobe Asabar bayan kammala wasan ƙungiyar tasa da Almeria, wanda zai zamo shine wasansa na ƙarshe a tarihi. Pique, mai shekaru 35, ya bayyana hakan ne a kafafensa na sadarwar zamani cikin wani bidiyo a jiya Alhamis. Ɗan wasan tsakiyar bayan dai sau uku kacal Barcelona ta saka shi a jerin ’yan wasa 11 na farko a kakar wasa ta bana, inda matasan ’yan wasa irinsu Ronald Araujo, Jules Kounde, Andreas Christensen da Eric Garcia suke…
Read More
Tsohon ɗan ƙwallon ƙafar Super Eagles da Kano Pillars, Bello Musa ya rasu

Tsohon ɗan ƙwallon ƙafar Super Eagles da Kano Pillars, Bello Musa ya rasu

Daga BASHIR ISAH Rahotanni sun ce Bello Musa Ƙofarmata ya rasu ne ranar Talata a mahaifarsa, Kano yana da shekara 34. Tuni aka yi jana'izar marigayin a Kano daidai da karantarwar Musulunci. Bayanai sun nuna Musa ya soma harkar ƙwallon ƙafa ne a 2007 a kulob ɗin Buffalo da ke Kano, daga bisani ya samu shiga ƙungiyar Kano Pillars. A 2010 ya sauya sheƙa zuwa ƙungiyar Heartland a Owerri sannan ya sake dawowa Kano Pillars a 2012, kana daga bisani ya tafi ƙungiyar Elkanemi Warriors a Maiduguri. Bayan wasu lokuta marigayin ya samu kwantiragi da kulob ɗin IK Start a…
Read More
An caccaki Ƙatar kan cin zarafin baƙi gabanin gasar Kofin Duniya

An caccaki Ƙatar kan cin zarafin baƙi gabanin gasar Kofin Duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu ƙasashe da babbar tawagar ƙwallon ƙafar Australiya sun caccaki jerin cin zarafin bil adama a Ƙatar, gabanin Gasar Kofin duniya da ke tafe a watan Nuwamban wannan shekarar, lamarin da ya sa Australiya kasance tawaga ta farko da ke cikin wannan gasa da ta caccaki ƙasar da ke karɓar baƙuncin gasar. Gasar Kofin Duniya da za a fara a ranar 20 ga watan Nuwamba ta fuskanci cece-kuce tun daga lokacin da aka bai wa Ƙatar damar karɓar baƙuncin shekaru 12 da suka wuce. Hukumar ƙwallon ƙafar Australia ta ce ta san cewa an yi sauye-sauye…
Read More
FA ta ci tarar kocin Liverpool Yuro 30,000

FA ta ci tarar kocin Liverpool Yuro 30,000

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar FA ta ci tarar kocin Liverpool, Jurgen Klopp Yuro 30,00 bayan jan katin a wasan da ƙungiyarsa ta yi nasara a kan Manchester City a ranar 16 ga watan Oktoba. An kori Klopp daga filin wasa bayan rashin ɗa'ar da ya yi wa mataimakin alƙalin wasa, lokacin da aka ƙi bai wa Mohamed Salah damar dukan da aka yi masa. Kocin ya nemi afuwa kan halayyar da ya nuna bayan an tashi daga wasa. "Wani abu ne ya ɗauki hankali ne, ba alfahari na ke ba. Na cancanci jan kati," a cewarsa. An tuhumi Klopp…
Read More
FIFA U17: Flamingos ta kai mataki na kusa da ƙarshe

FIFA U17: Flamingos ta kai mataki na kusa da ƙarshe

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Mata ta Nijeriya (Flamingos) ta samu nasarar tsallakewa zuwa mataki na kusa da ƙarshe na gasar Kofin Duniya na FIFA na mata 'yan ƙasa da shekara 17 wanda ke gudana a Indiya. Flamingos ta samu wannan nasara ne bayan da ta lallasa takawararta ta Amurka da ci 4-3 a bugun fenariti. An buga wannan wasa ne a ranar Juma'a, 21 ga Oktoba, 2022.
Read More
Yadda Benzema ya lashe kyautar Ballon d’Or na bana

Yadda Benzema ya lashe kyautar Ballon d’Or na bana

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A cikin makon nan ne fitaccen ɗan wasan ƙungiyar Real Madrid, Karim Benzema ya lashe kyautar Ballon d'Or ta Gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa ta duniya na 2022, yayin bikin da ya gudana a birnin Paris, inda ya gaji Lionel Messi wanda ya lashe kyautar a bara. A shekarar bana dai, Paris babban birnin Faransa ya zama na musamman ga ɗan wasan gaban na Real Madrid, domin kuwa a nan ne, suka lashe kofin gasar Zakarun Turai karo na 14, bayan doke Liverpool da 1-0 a watannin baya. Ƙididdiga ta nuna cewar, sau goma sha biyu…
Read More
Man United za ta daƙile yunƙurin FA na dakatar da Ronaldo

Man United za ta daƙile yunƙurin FA na dakatar da Ronaldo

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Manchester United ta ce za ta ɗauki dukkanin matakan da suka dace wajen daƙile yunƙurin hukumar FA game da shirinta na dakatar da ɗan wasan gaban ƙungiyar Cristiano Ronaldo, bayan abin da ya faru a filin wasa na Goodison Park cikin watan Aprilun da ya gabata. Mai horar da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United, Erik ten Hag ya ce ɗan wasan gaban na Portugal ba zai lamunce duk wani rashin adalci daga hukumar ta FA ba. Cristiano Ronaldo wanda ’yan sanda suka aikewa da takardar gargaɗi ya na da zavin daga…
Read More
Salah ya kafa tarihin zura ƙwallaye uku cikin sauri a gasar Zakarun Turai

Salah ya kafa tarihin zura ƙwallaye uku cikin sauri a gasar Zakarun Turai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan gaba na ƙungiyar Liverpool Mohamed Salah ya kafa tarihin shiga sahun waɗanda suka yi nasarar cin ƙwallaye 3 a wasa guda cikin sauri a gasar kofin zakarun Turai, bayan da ya zura ƙwallayen 3 wato 'hattrick' cikin mintuna 6 da shiga fili a karawarsu da Rangers daren Laraba. Ƙwallayen na Salah dai ya goge tarihin Bafetimbo Gomis na Lyon wanda ya taɓa nasarar zuwa ƙwallaye 3 cikin mintuna 8 yayin wasansu da Dinamo Zagreb a 2011 ƙarƙashin makamanciyar gasar Yayin wasan na daren Laraba da ya gudana a Ibrox Liverpool ta tashi wasa 7…
Read More
Ronaldo na da damar tafiya a duk lokacin da ya so – Man United

Ronaldo na da damar tafiya a duk lokacin da ya so – Man United

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United ta ce ta na a shirye idan har Cristiano Ronaldo zai sake jarraba barin ƙungiyar a watan Janairu, idan har ɗan wasan gaban ya gaza samun wuri a tawagar Erik Ten Hag, kamar yadda wasu majiyoyi suka bayyana. Ronaldo mai shekaru 37 ya yi zaman benci a wasan da Man United suka sha kashi 6-3 a hannun Man City a wasan hamayya da suka gwabza a gasar Firmiyar Ingila a ƙarshen makon da ya wuce, haka zalika bai fara a wasan da suka yi rashin nasara 4-0 a hannun Brentford…
Read More
Akwai matsala a tsaron bayan Liverpool – Klopp

Akwai matsala a tsaron bayan Liverpool – Klopp

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mai horar da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool, Jurgen Klopp ya amsa cewa dole ne tawagarsa ta sake lale, tare da ƙara ƙaimi a kan yadda ta ke tsaron baya, dai dai lokacin da ƙungiyar wadda ta ƙarƙare a matsayin ta biyu a kakar da ta gabata, ga fama da rashin nasara a wannan kaka. Liverpool wadda yanzu haka ke matsayin ta 9 a teburin gasar Firimiya, bayan nasara a wasanni 2 kacal daga cikin 7 da ta doka a wannan kaka. Ƙungiyar dai na ci gaba da shan caccaka musamman daga magoya baya, ganin yadda…
Read More