Wasanni

Gareth Bale ya fice daga Madrid zuwa MLS

Gareth Bale ya fice daga Madrid zuwa MLS

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rahotanni daga Birtaniya da Amurka sun nuna cewa, Gareth Bale ya koma Los Angeles FC bayan ya bar Real Madrid. Jaridar Los Angeles Times, ta nakalto majiyar Major League Soccer tare da sanin yarjejeniyar ta ce, tauraron mai shekaru 32 zai iya buga wasa a LAFC daga ranar 1 ga watan Yuli. A halin da ake ciki, ESPN ta ruwaito cewa, Bale zai tashi zuwa Los Angeles a ƙarshen mako mai zuwa don sanya hannu kan yarjejeniyar da za ta ƙare a ƙarshen kakar wasa ta bana, tare da zaɓin ƙarin shekara. Bale ya taɓa zama…
Read More
Super Eagles ta koma matsayi na 31 a jadawalin FIFA

Super Eagles ta koma matsayi na 31 a jadawalin FIFA

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta koma matsayi na 31 a sabon jadawalin FIFA da aka fitar a ranar Alhamis. An buga sabon matsayi na ne akan gidan yanar gizon FIFA. A Afirka, Super Eagles yanzu ta koma matsayi na huɗu bayan Senegal da Morocco da Tunisia, waɗanda ke matsayi na ɗaya da na biyu da na uku. Saliyo wadda ta yi rashin nasara a hannun Eagles a wasannin neman cancantar shiga gasar AFCON ta 2023, ta koma mataki na 113 yayin da Guinea-Bissau ta kasance a matsayi na 115. Sao Tome and Principe, wacce ta…
Read More
Yadda ’yan wasa da magoya bayansu suka fusata suka kashe alƙalin wasa

Yadda ’yan wasa da magoya bayansu suka fusata suka kashe alƙalin wasa

Wani alƙalin wasa ɗan ƙasar Salvadoriya ya gamu da ajalinsa sakamakon raunukan da ya samu a wani harin da ’yan wasa da magoya bayansu suka kai masa. Jose Arnoldo Amaya ya kasance yana jagorantar wani wasa a makon da ya gabata, kuma ya nuna katin gargai na biyu ga wani ɗan wasa, inda ya kore shi saboda rashin ɗa'a. Abin mamaki, wannan ya sa 'yan wasa da magoya bayansu suka yi wa ɗan shekaru 63 ɗin mummunan duka, daga bisani kuma ya mutu sakamakon zubar jini na ciki. Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Salvadoran dai ta yi gaggawar fitar da wata…
Read More
AFCON 2023: Nijeriya ta lallasa Sao Tome da ci 10-0

AFCON 2023: Nijeriya ta lallasa Sao Tome da ci 10-0

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A cigaba da buga wasannin neman cancantar buga kofin nahiyar Afirka (AFCON), tawagar Nijeriya ta Super Eagles ta lallasa takwararta ta Sao Tome da Principe da ci 10 ba ko ɗaya. A wasan dai wanda aka fafata ranar Litinin, ɗan wasan Nijeriya Victor Osimhen ne ya ci wa Super Eagles ƙwallo huɗu shi kaɗai. Osimhen ya fara zura wa Nijeriya ƙwallo ta farko ne a minti na tara da fara wasan, kafin ya taimaka wa Moses Simon da Terem Moffi su ma su zura nasu ƙwallayen a mintuna na 28 da na 43. Ya kuma ƙara…
Read More
Sojoji sun shirya gasar ƙwallon ƙafa ta zaman lafiya a Kudancin Kaduna

Sojoji sun shirya gasar ƙwallon ƙafa ta zaman lafiya a Kudancin Kaduna

Daga WAKILINMU Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Zonkwa Selected da ke Ƙaramar Hukumar Zangon Kataf a Jihar Kaduna, ta lashe gasar ƙwallon ƙafa ta zaman lafiya da rundunar kiyaye zaman lafiya 'Operation Safe Haven' ta shirya a Kudancin Kaduna. Ƙungiyar dai ta lashe gasar ce bayan ta lallasa takwararta ta Golden Balley da ke Ƙaramar Hukumar Jama’a da ci 3-1 a wasan ƙarshe da aka buga a sabon filin wasa na garin Kafanchan a da ke Jihar Kaduna. Da ya ke jawabi bayan kammala gasar, Kwamandan Rundunar ta OPSH mai hedkwata a Jos, babban birnin Jihar Filato, Manjo Janar Ibrahim Sallau…
Read More
Ina alfahari da Super Eagles duk da rashin nasara a hannun Mexico – Peseiro

Ina alfahari da Super Eagles duk da rashin nasara a hannun Mexico – Peseiro

Jose Peseiro, sabon kocin Super Eagles, ya bayyana cewa, yana alfahari da ƙungiyar duk da rashin nasarar da suka yi a hannun Mexico da ci 2-1 a wasan sada zumunci da sanyin safiyar Lahadi. Har ila yau 'yan wasan na Portugal sun yaba wa ’yan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya (NPFL), saboda rawar da suka taka a wasan. “Ko da ya ke ba mu yi nasara ba a daren jiya, ina matuƙar alfahari da yaran,” Peseiro ya rubuta a shafin sa na twitter. “Ƙungiyar ta nuna hali da juriya. Magana ta musamman ga ’yan wasan NPFL huɗu da suka…
Read More
Mata zai bar Man United a ƙarshen watan Yuli

Mata zai bar Man United a ƙarshen watan Yuli

Juan Mata zai bar Manchester United a matakin wanda bai da ƙungiyar, idan yarjejeniyarsa ta ƙare a ƙarshen kakar bana. Mai shekara 34, wanda ya taka rawar da ta kai Sifaniya ta lashe kofin duniya a 2010, ya koma United daga Chelsea a 2014 kan fam miliyan 31.1. Mata wanda ya ci ƙwallo 51 a wasa 285 da ya yi wa United, ya buga Premier League ta bakwai a kakar nan da aka kammala ranar 22 ga watan watan Mayu. Ranar Laraba, Manchester United ta sanar da cewar Paul Pogba, wanda kwantiraginsa zai ƙare a bane, zai bar Old Trafford.…
Read More
PSG ta yi wa Real Madrid yankan baya ta cigaba da riƙe Mbappe

PSG ta yi wa Real Madrid yankan baya ta cigaba da riƙe Mbappe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan gaba na ƙungiyar PSG a ƙasar Faransa, Kylian Mbappe ya yanke hukuncin cigaba da zama a ƙungiyar bayan kwashe makonni ana danganta shi da tafiya ƙungiyar Real Madrid ta ƙasar Spain. Jaridar L’Equip da ke Faransa da Marca da ke Spain sun ruwaito cewa, Mbappe ya yanke hukucin zama a PSG da kuma rattaba hannu akan wata sabuwar kwangilar shekaru 3 idan wa’adin kwangilar sa ta yanzu ta ƙare a ranar 30 ga watan Yuni mai zuwa. Wakilan Mbappe sun ƙi yin bayani akan sabuwar kwangilar da PSG za ta ba shi, sai dai…
Read More
An fitar da kulab ɗin da ‘yan wasan Nijeriya biyar ke buga ƙwallo a Firimiyar Ingila

An fitar da kulab ɗin da ‘yan wasan Nijeriya biyar ke buga ƙwallo a Firimiyar Ingila

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An fitar da Watford daga gasar firimiya bayan da Wilfried Zaha ya buge bugun daga kai sai mai tsaron gida wanda Crystal Palace ta yi nasara a Selhurst Park. Mataimakin kyaftin ɗin Super Eagles na Nijeriya William Troost Ekong yana taka leda a Watford. Wasu ’yan wasan Super Eagles huɗu da suka haɗa da Oghenekaro Etebo, Samuel Kalu, Maduka Okoye da Bonaventure Dennis duk suna cikin tawagar Watford. Nasarar da Burnley ta yi a makon da ya gabata ya bar Hornets da maki 12 yayin da ya rage saura wasanni huɗu kuma Palace ta aika da…
Read More
Zan iya cigaba da zama kocin Madrid shekaru 10 – Ancelotti

Zan iya cigaba da zama kocin Madrid shekaru 10 – Ancelotti

Kocin Real Madrid Carlo Ancelotti ya bayyana cewa, wataƙila ya yi ritaya idan ya bar ƙungiyar da ta zama zakarar gasar La Liga a bana, sai dai ya ce, a shirye ya ke ya cigaba da zama tare da qungiyar Madrid ɗin tsawon shekaru masu yawa a nan gaba. Ancelotti ɗan ƙasar Italiya mai shekaru 62 a duniya, ya zama koci na farko a tarihi da ya lashe kofunan manyan lig-lig guda biyar na Turai, nasarar da ya cimma a wannan kakar tare da Real Madrid bayan lashe gasar La Liga, inda kuma ya jagoranci karawa da Manchester City ranar…
Read More