Wasanni

AFCON: Buhari ya taya ‘yan wasan Super Eagles murna

AFCON: Buhari ya taya ‘yan wasan Super Eagles murna

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya bayyana jin daɗinsa tare yaba wa 'yan wasan Super Eagles dangane da nasarorin da suka samu a duka wasanni ukun da suka buga a gasar cin kofin Afirka (AFCON) da ke gudana a ƙasar Kamaru. Buhari ya nuna jin daɗinsa ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na facebook a ranar Laraba. Buhari ya buƙaci 'yan wasan da su ci gaba da tabbata a kan wannan hanya ta nasara da suka ɗauka har zuwa ƙarshen gasar tare kuma da zama jakadu nagari ga Nijeriya a cikin filin wasa da kuma wajen…
Read More
Ɗan wasan Madrid, Isco, na shirin ƙulla yarjejeniya da Barcelona

Ɗan wasan Madrid, Isco, na shirin ƙulla yarjejeniya da Barcelona

A karon farko cikin kusan shekaru 15, ana shirin samun sauyin sheƙar ɗan wasa kai tsaye tsakanin manyan abokan hamayya a gasar La Liga, wato Real Madrid da Barcelona FC. Rabon da a ga irin wannan sauyin sheƙa dai tun shekara ta 2007, lokacin da Javier Saviola ya koma Real Madrid daga Barcelona. A halin yanzu kuma ɗan wasan tsakiyar Real Madrid, Isco Alcaron, ke shirin sauyin shekar zuwa Camp Nou. Tuni dai aka tsegunta cewar har ma Isco ya gana da kocin Barcelona Xavi Hernandez. Ɗan wasan mai shekaru 29 a yanzu shi ne na 5 a matakin muhimmanci…
Read More
Yadda Nijeriya ta lallasa Masar a gasar AFCON

Yadda Nijeriya ta lallasa Masar a gasar AFCON

Daga WAKILINMU Kelechi Iheanacho na Super Eagles ya cirewa Nijeriya kitse a wuta a karawarta da Masar ranar talata bayan ƙwallonsa da ta bai wa ƙasar ta yammacin Afrika nasara a wasanta na farko ƙarƙashin gasar cin kofin Afrika. Shahararren ɗan wasan gaba na Liverpool Salah bai taɓuka abin kirki ba, sakamakon yadda zaratan ’yan wasan Nijeriya suka riƙe shi tsawon mintuna 90 da aka yi a wasan. Babban wasa na biyu da kowa ke jiran gani a gasar cin kofin Afrika na shekarar 2021 tsakanin Nijeriya da Misra, ya zo ƙarshen inda Nijeriya ta yiwa Misra da shahararren ɗan…
Read More
Korona: Kashi 60 za a bari su shiga kallon gasar Kofin Afrika

Korona: Kashi 60 za a bari su shiga kallon gasar Kofin Afrika

Daga WAKILINMU A tsakanin watannin Yuni da Yulin bara ya kamata a yi gasar, amma annobar Korona ta sa aka ɗage zuwa bana. Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta nahiyar Afirka CAF ta ce kashi 60 zuwa 80 na ’yan kallo za a bari su shiga filayen wasanni da za a kara gasar cin kofin nahiyar na AFCON. Matakin a cewar hukumar na da nasaba da annobar COVID-19. Cikin wata sanarwa da ta fitar, CAF ta ce bayan wata tattaunawa da ta yi da hukumomin cikin gida na Kamaru, sun cimma matsaya akan cewa kowanne filin wasa za a bar ‘yan kallo…
Read More
Hana Ighalo wakiltar Nijeriya: Eguavoen ya mayar da martani ga Al-Shabab

Hana Ighalo wakiltar Nijeriya: Eguavoen ya mayar da martani ga Al-Shabab

Daga WAKILINMU Kocin riƙon ƙwarya na Super Eagles, Augustine Eguavoen, ya ce, yana da ƙwarin gwiwar cewa Odion Ighalo zai haɗa kai da sauran ‘yan wasan da za su buga gasar kofin Afrika ta 2021. Ƙungiyar Al Shabab ta Ighalo ta ƙi sakinsa a domin fafata gasar. Wannan ya sa tsohon ɗan wasan Manchester United da Watford ya shiga tsakanin kulob da ƙasar. An ruwaito Ighalo yana Nijeriya kuma yana da wa’adin tabbatar da kasancewarsa. “Da fatan Odion ya zo,” inji Eguavoen a wani taron manema labarai a ranar Talatar da ta gabata. Ana kyautata zaton cewa gogaggen ɗan wasan…
Read More
Nijeriya ta naɗa Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles

Nijeriya ta naɗa Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles

Daga WAKILINMU Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) ta bayar da sanarwar naɗa Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles a ranar Laraba. Hukumar ta ce, Jose Peseiro wanda ɗan asalin ƙasar Portugal ne shi zai maye gurbin Gernat Rohr da ta kora. Tuni NFF ta naɗa Augustine Eguavoen a matsayin kocin riƙon ƙwarya domin ya ja ragamar Super Eagles a yayin da ake shirin soma gasar cin kofin Afirka. A cikin sanarwar da ta fitar NFF ranar Laraba ta ce kwamitin zartarwata ne ya amince da naɗa Peseiro ne bayan raba gari da Gernot Rohr. “Kwamitin ya amince…
Read More
An zaɓi Samuel Eto’o ya zama shugaban hukumar ƙwallon ƙafa na Kamaru

An zaɓi Samuel Eto’o ya zama shugaban hukumar ƙwallon ƙafa na Kamaru

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An zaɓi shahararren ɗan ƙwallon Kamaru, Samuel Eto’o a matsayin shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasa (FECAFOOT) a ranar Asabar, wata ɗaya kafin ƙasar ta karɓi baƙuncin gasar cin kofin Afrika. Tsohon ɗan wasan gaba Eto’o, wanda ya taka leda a Barcelona, Inter Milan da Chelsea, zai karɓi ragamar ƙungiyar da ta daɗe tana fama da rigingimu, rashin gudanar da mulki da kuma zargin cin hanci da rashawa. Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA ta shiga tsakani sau da yawa don kawo ƙarshen cece-kuce tsakanin jami'an FECAFOOT. Eto’o mai shekaru 40 ya lashe zaɓen da ƙuri’u…
Read More
Da alamu matar Cristiano Ronaldo ta harbu

Da alamu matar Cristiano Ronaldo ta harbu

Fostin ɗin da ɗan wasa Cristiano Ronaldo ya wallafa a shafinsa na Instagram na cewa matarsa ta samu 'juna biyu. Wannan shi ne fostin na farko da wani ɗan wasa a duniya ya samu mabiya (Likes) mutum miliyan 27 da dubu ɗari ɗaya, kuma yana ci gaba da ƙaruwa ahalin yanzu ashafin Instagram. Ba a iya ƙwallon ƙafa ba, a kowane irin wasa a duniya babu wani ɗan wasa da ya taɓa samun yawan mabiya da suka kai na waɗanda suka bibiyi fostin ɗin na Cristiano Ronaldo wanda ya wallafa a jiya tare da shi da matarsa Georgina.
Read More
A karon farko za a fara gasar daddalla mari a Nijeriya

A karon farko za a fara gasar daddalla mari a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Masu shirya wata sabuwar gasa da za a fara a karon farko a Nijeriya, sun ce a fito a fafata domin za a fara gasar mare-mare cikin watan Oktoba a Nijeriya. Babban Daraktan kamfanin tsara wasannin na TKK Sports, Abdulrahman Orosanya ne ya bayyana haka, ranar Juma’a a Legas. Ya ƙara da cewa, ba a dai sa ranar da za a fara ba, amma dai cikin watan Oktoba za a fara, kuma a cikin Disamba za a yi wasannin ƙarshe na cin kofuka. Orosanya ya ce, an ƙirƙiro wannan wasan daddalla mari a ƙasar Rasha, amma…
Read More
Gwamna Sule ya zira ƙwallo a raga a wasan bikin cikar Nasarawa shekara 25 da kafuwa

Gwamna Sule ya zira ƙwallo a raga a wasan bikin cikar Nasarawa shekara 25 da kafuwa

Daga BASHIR ISAH A matsayin wani ɓangare na cikar Jihar Nasarawa shekara 25 da kafuwa, gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abdullahi Sule, ta shirya wasan ƙwallon ƙafa na sada zumunta inda aka fafata tsakanin ɓangaren Gwamna Sule da ya ƙunshi tsoffin masu buga wa jihar wasa, da kuma ɓangaren tsoffin 'yan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙsa, wato Super Eagles. Sanarwar da ta fito ta hannun jami'in yaɗa labarai na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Nasarawa United, Eche Amos, ta nuna an buga wannan wasa ne a ranar Alhamis da ta gabata a babban filin wasannin motsa jiki da ke Lafia…
Read More