Wasanni

Diawara ya soke kwataraginsa da Faransa bayan haramta wa ’yan wasa yin azumi

Diawara ya soke kwataraginsa da Faransa bayan haramta wa ’yan wasa yin azumi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ƙasar Faransa ta gayyaci Dehmaine Tabibou Assoumani na ƙungiyar Nantes a matsayin wanda zai maye gurbin ɗan wasan tsakiyar tawagar ’yan ƙasa da shekara 19 ta ƙasar. Ɗan wasan tsakiyar Mahamadou Diawara ya yanke shawarar barin tawagar ne bayan da hukumar ƙawallon ƙafa ta ƙasar ta kafa wasu sabbin dokoki waɗanda suka haramtawa 'yan wasa Musulmi yin azumin watan Ramadan a lokacin da suke atisaye. Diawara bai ji dadin sabbin dokokin ba, waɗanda aka fara aiwatar da su tun daga matakin tawagar ’yan qasa da shekaru 16 har zuwa babbar tawagar ƙasar. Wannan…
Read More
Zan bayyana makomata bayan gasar kofin Turai – Mbappe

Zan bayyana makomata bayan gasar kofin Turai – Mbappe

Sga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan gaba na PSG Kylian Mbappe ya ce zai bayyana matsayarsa na gaba bayan gasar kofin nahiyar Turai ta 2024. Ɗan wasan na Faransa ya yi magana a karon farko game da raɗe-raɗin da ake yi na yarjejeniyarsa da Real Madrid a bazara. A yayin da yake magana a gidan jaridar Faransa, ya ce “Ban sanar da komai ba saboda babu abin da zan sanar. "Zan bayyana makomata kafin gasar kofin Turai." Dangane da gasar Olympics ta Paris, Mbappe ya ce: “A koyaushe ina da wannan buri, abu ne na musamman kuma a koyaushe ina…
Read More
Amusan ta lashe tambarin zinare a gasar tseren Afrika

Amusan ta lashe tambarin zinare a gasar tseren Afrika

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sarauniyar wasannin guje-guje ta Nijeriya, Tobi Amusan, ta cika burin magoya bayanta bayan da ta lashe tambarin zinare a tseren gudu na mita 100 a gasar kofin Afrika da ke ci gaba da gudana a ƙasar Ghana. Amusan, wadda ita ce ke riƙe da kambun tseren mita 100 na duniya, ta kasance wadda aka fi so a gasar, an nuna mata ƙauna bayan ya doke sauran abokan hamayyarta a karo na farko a tsaren. A karo na biyu bayan an harba bindigar farawa, Amusan ba ta tsaya sanya ba, inda ta yi nasara a cikin sauƙi…
Read More
Gasar Zakarun Turai: Arsenal da Barcelona sun kai zagayen kusa da ƙarshe

Gasar Zakarun Turai: Arsenal da Barcelona sun kai zagayen kusa da ƙarshe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Arsenal ta kai zagayen daf da na kusa da na ƙarshe, bayan da ta yi nasara a kan FC Porto da cin 4-2 a bugun fenariti ranar Talata a Emirates. Tun farko Arsenal ce ta ci 1-0 ta hannun Leandro Trossard saura minti hutu su je hutu, irin wannan sakamakon Porto ta samu a Portugal a wasan farko. Hakan ne ya sa aka yi ƙarin lokaci daga nan aka je bugun daga kai sai mai tsaron raga. Gunners ta ci ƙwallaye a bugun fenariri ta hannun Odegaard da Kai Havertz da Bukayo Saka da kuma Declan…
Read More
An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kamaru ta dakatar da 'yan wasan ƙasar 62 bisa laifin coge wajen bayyana shekaru, cikinsu har da matashi mafi ƙarancin shekaru a tawagar da ta buga gasar kofin nahiyar Afirka da aka yi a watan Janairu. Hukumar ta FECAFOOT ta fitar da jerin sunayen a hukumance a ƙarshen wannan makon, ciki harda Wilfried Nathan Douala mai shekaru 17 wanda ya ba da mamaki cikin tawagar Rigobert Song a gasar da aka kammala a Ivory Coast. A cewar FECAFOOT, mai tsaron ragar Victoria United ya yi ƙarya game da shekarunsa, don haka an hana…
Read More
La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

Daga MAHDI M. MUHAMMAD La Liga na nazarin wani bidiyo da ake zargin yana nuna wariyar launin fata ga Vinicius Jr a wasan da Real Madrid ta buga da Valencia a ƙarshen makon da ya gabata. Bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta na Intanet ya nuna yadda wani yaro mai goyon bayan Valencia ke jagorantar cin zarafin ɗan wasan. Vinicius ya zura ƙwallaye biyu a wasan da suka tashi 2-2 a ranar Asabar kuma ya yi murna ta hanyar ɗaga hannunsa sama. Ɗan wasan mai shekaru 23 ya fuskanci cin zarafi na wariyar launin fata sau da dama…
Read More
Ahmed Musa ya dakatar da kwantiraginsa da Sivasspor ta Turkiyya

Ahmed Musa ya dakatar da kwantiraginsa da Sivasspor ta Turkiyya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rahotanni sun bayyana cewa kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa ya soke kwantiraginsa da ƙungiyar Sivasspor ta Turkiyya. An kawo ƙarshen kwantiragin tsakanin Musa da Sivasspor ta hanyar yarjejeniya. Ɗan wasan mai shekaru 31 ya ɗauki matakin ne bayan ƙungiyar ta kasa biyan albashin sa na watanni shida da suka gabata. Ɗan wasan gaba ya riga ya fara aiki don komawa wani kulob a lokacin bazara. Musa ya koma Sivasspor daga wata ƙungiyar Turkiyya Fatih Karagumruk a shekarar 2022. Ya buga wasanni tara a ƙungiyar ba tare da samun nasarar zura ƙwallo ko ɗaya a raga…
Read More
Rashin ɗa’a: An dakatar da Ronaldo wasa ɗaya a Al-Nassr

Rashin ɗa’a: An dakatar da Ronaldo wasa ɗaya a Al-Nassr

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An dakatar da ɗan ƙwallon Al-Nassr Cristiano Ronaldo daga buga wasa ɗaya saboda tanka wa ’yan kallo a wasan da suka doke Al-Shabab a gasar ƙwallon Saudiyya. Magoya bayan Al-Shaabab sun yi ta ihun sunan 'Messi', mutumin da ya kasance babban abokin hamayyar Ronaldo. Al-Nassr ta samu nasara a wasan da ci uku da biyu a birnin Riyadh. Kyaftin ɗin Portugal mai shekaru 39, ya rufe kunnensa sannan ya yi wata alama da hannu. Hukumar ƙwallon Saudiyya - SAFF ta kuma ci tarar Ronaldo ɗin Riyal dubu 30. Kwamitin ɗa'a na ƙwallon Saudiyyar ya ce Ronaldo…
Read More
Kocin Super Eagles, Jose Peseiro ya yi murabus

Kocin Super Eagles, Jose Peseiro ya yi murabus

Daga BASHIR ISAH Jose Peseiro ya murabus a matsayin mai horar da 'yan wasan Super Eagles na Nijeriya. Peseiro ya sanar da hakan ne a shafinsa na X a ranar Juma'a, 1 ga Maris, 2024. Ya ce kwatiraginsa da Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) ta ƙare, kuma ba a ƙulla sabo ba. Ya bayyana watanni 22 da ys shafe a matsayin babban kocin Super Eagles, a matsayin sadaukarwa. Ya kuma yi amfani da wannan dama wajen nuna godiya ga 'yan wasan na Super Eagles da hukumar NFF, yana mai cewa a duk lokacin da aka buƙace za a same…
Read More
Kocin Bayern, Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana

Kocin Bayern, Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Koci Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar Bayern Munich a ƙarshen kakar wasa ta bana. Ɗan shekaru 50 ɗin ya maye gurbin Julian Nagelsmann a watan Maris din 2023, inda ya ƙulla yarjejeniyar har zuwa watan Yunin 2025. Sai dai tsohon kocin Chelsea ɗin zai raba gari da ƙungiyar saboda "sauye-sauyen da Bayern ke yi". Tuchel ya jagoranci Bayern lashe gasar Bundesliga a kakar wasan da ta wuce amma a yanzu Bayer Leverkusen ta basu tazarar maki takwas. Sannan kuma an doke Bayern a wasa uku a jere. Shugaban Bayern, Jan- Christian Dreesen ya ce "duka ɓangarorin…
Read More