Wasanni

Yadda Kano Pillars ta fara gasar firimiyar Nijeriya da kafar dama

Yadda Kano Pillars ta fara gasar firimiyar Nijeriya da kafar dama

Kano Pillars ta yi nasarar doke Ikorodu United 3-0 ranar Lahadi a wasan makon farko da fara gasar firimiyar Nijeriya ta 2024/25. Pillars ta buga wasan ne a jihar Katsina, bayan da ake gyaran filin wasanta na Sani Abacha da ke kofar Mata a Kano, Nijeriya. Pillars ta ci ƙwallayen ta hannun Mustapha Umar da Rabiu Ali da ya zura biyu a raga, mai shekara 43 yana buga kaka ta 18 a babbar gasar tamaula ta Nijeriya. Da wannan sakamakon Pillars, wadda ake kira sai masu gida tana ta ɗaya a kan teburi da maki uku, sai Sunshine Stars ta…
Read More
Yadda ’yan Nijeriya suka lashe zinare da tagulla a gasar Paralympics

Yadda ’yan Nijeriya suka lashe zinare da tagulla a gasar Paralympics

'Yar wasan ɗaga abu masu nauyi Onyinechi Mark ta yi nasarar lashe lambar zinariya a gasar wasannin Paralympics ta masu nakasa da ke gudana a Faransa. Onyinechi ta ci zinariyar ne a ajin nauyin 61kg, inda ta ɗaga nauyin 150kg a makon da ya gabata a birnin Paris. Ita ce ’yar wasa ta farko da ta ci wa Nijeriya zinariya a wasannin bana. Nijeriya ba ta ci kyauta ko ɗaya ba a gasar Olympics da aka kammala. Da ma ita ce ke riƙe da tarihi a wannan ajin a duniya baki ɗaya. Hakazalika, wata ’yar wasan Nijeriya, Flora Ugwunwa ta…
Read More
Fitacciyar ’yar wasan Olympics ta mutu bayan saurayinta ya banka mata wuta

Fitacciyar ’yar wasan Olympics ta mutu bayan saurayinta ya banka mata wuta

’Yar wasan Olympics ta ƙasar Uganda, Rebecca Cheptegei, ta mutu bayan da tsohon saurayinta ya zuba mata fetur ya kuma banka mata wuta. ’Yar tseren gudun mai shekara 33, wadda ta fafata a birnin Paris, ta samu ƙona sosai a duk jikinta. Hukumomi a arewa maso yammacin Kenya, inda Cheptegei ke zaune sun ce lamarin ya faru ne bayan da ta koma gida daga coci. Hukumomin ƙasar sun yi imanin cewa Rebecca da tsohon saurayinta na ta taƙaddama kan wasu filaye. ’Yar wasan ta rasu sakamakon ƙunan, yayin da tsohon saurayin nata shi ma ya samu ɗan ƙuna kuma yana…
Read More
Suarez ya yi ritaya daga buga wa Uruguay wasa

Suarez ya yi ritaya daga buga wa Uruguay wasa

Luis Suarez ya sanar da yin ritaya daga buga wa tawagar Uruguay ƙwallon ƙafa. Mai shekara 37 ya ɓarke da kuka a lokacin da ya ce wasan da ƙasar za ta kara da Paraguay a neman shiga kofin duniya ranar Asabar, shi ne na ƙarshe da zai yi. Tsohon ɗan wasan Liɓerpool da Barcelona shi ne kan gaba a yawan ci wa kasar ƙwallaye mai 69 a raga a karawa 142 - ya fara taka mata leda a Fabrairun 2007 a karawa da Colombia. Suarez ya buga wa Uruguay manyan gasa tara a faɗin duniya. An yi masa jan kati…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Casemiro ya shirya tsaf domin ƙin amsa tayin kowacce ƙungiya, saboda ya lashi takobin mayar da martabarsa da ci gaba da kasancewa a Man United. Newcastle ta haƙura da nacin ɗauko mai tsaron gida na Ingila, da ke taka leda a Crystal Palace Marc Guehi 25, domin nunawa ƙungiyar ba za a yi amfani da su idan an buɗe kasuwar musayar 'yan wasa ba. Mai tsaron gida na Sifaniya da ke taka leda a Real Madrid Dani Carɓajal, mai shekara 32, ya ce akwai yiwuwar zai buga ƙwallom ƙafa a Amirka kafin ya yi ritaya daga buga ƙwallo. Everton na…
Read More
 D’Tigress ta shiga jerin ƙwararrun ƙungiyoyin ƙwallon kwando 10 na duniya

 D’Tigress ta shiga jerin ƙwararrun ƙungiyoyin ƙwallon kwando 10 na duniya

Hukumar ƙwallon Kwando ta Duniya (FIBA) ta bayyana cewa, ƙungiyar ƙwallon ƙwando ta Mata ta Nijeriya, D’Tigress, ta hau matsayi na takwas a jerin ƙasashe na duniya bayan rawar da ta taka a Gasar wasannin Olympics na 2024 a Paris. A ranar Alhamis FIBA ta fitar da jerin sunayen ƙasashen. Wannan ƙarin matsayi ya tabbatar da matsayinsu a cikin manyan ƙungiyoyi goma na duniya, wanda ya sa suka zama ƙungiyar Afirka ta farko, maza ko mata, da ta kai wannan matsayi a jerin ƙasashe na duniya na FIBA. ƙungiyar ta D’Tigress, it ace ta farko a nahiyar Afirka da ta…
Read More
Ban tattauna da wata ƙungiya ba a kan barin Man City – De Bruyne

Ban tattauna da wata ƙungiya ba a kan barin Man City – De Bruyne

ɗan wasan ƙungiyar Manchester City, Keɓin Bruyne ya bayyana cewa shi bai magana da wata ƙungiya ba a kan barin ƙungiyar a bana. ɗan wasan na ƙasar Belgium ya bayyana cewa "ƙofarsa a buɗe take" sannan ya tattauna da iyalansa a kan yiwuwar barin Manchester City bayan an bayyana cewa wasu ƙungiyoyin a Saudiya na zawarcinsa a ƙarshen kakar bara. De Bruyne mai shekara 33 ya koma Manchester City ne a shekarar 2015 daga Wolfsburg ta Jamus, shekara ɗaya gabanin zuwa Pep Guardiola. Gurdiola ya sha bayyana a watannin baya cewa ba za su sayar da De Bruyne ba, sannan…
Read More
Sabon jadawalin gasar zakarun Turai na 2024/25

Sabon jadawalin gasar zakarun Turai na 2024/25

Gasar zakarun nahiyar Turai ta dawo a wannan kaka ta 2024/2025, amma ba kamar yadda yake a baya ba, saboda an samu sauyi sosai. Wasu sauye-sauyen dai masu sauƙin fahimta ne, wasu kuwa akwai sarƙaƙiya. Da farko dai wannan ne karo na farko a cikin shekaru 21 da aka sau sauyi a tsarin gasar zakarun Turai. Daga shekaru 21 da suka wuce zuwa wannan kaka, ƙungiyoyi 32 ne ke fafatawa a wannan gasa, kuma an kasa su ne zuwa cikin rukunnai 8 mai ƙunshe da tawaga 4 ko wanne. Tawagogi 2 da suka fi samun maki a kowane rukuni su…
Read More
’Yar Nijeriya mai shekaru 18 Eniola Bolaji ta kafa tarihi a gasar Paralympics

’Yar Nijeriya mai shekaru 18 Eniola Bolaji ta kafa tarihi a gasar Paralympics

Eniola Bolaji mai shekaru 18 ta kafa tarihi kuma ta lashe lambar yabo ta farko a matsayin ’yar Nijeriya a gasar Paralympics ta 2024. Eniola ta kafa tarihi a matsayin 'yar wasa ta farko a Afirka da ta samu lambar yabo a wasan Para-Badminton bayan ta samu lambar tagulla ga Nijeriya a rukunin mata na Singles SL3. A safiyar ranar Litinin, Bolaji ta doke abokiyar karawarta ta Ukrainian, Oksana Kozyna, da ci 2-0 (21-9, 21-9) ta lashe lambar yabo ta farko a gasar Paralympics a matsayin 'yar Nijeriya a birnin Paris. Bolaji ya ci ƙwallayen biyun da ci 21-9 iri…
Read More
Ɗan wasan Nijeriya na farko a gasar Olympic Nojim Maiyegun ya mutu

Ɗan wasan Nijeriya na farko a gasar Olympic Nojim Maiyegun ya mutu

Fitaccen ɗan wasan Nijeriya na farko a gasar Olympics, Nojim Maiyegun ya mutu yana da shekaru 84 a duniya. Maiyegun ya kafa tarihi inda ya lashe lambar tagulla a dambem masara nauyi a gasar Olympics ta Tokyo a shekarar 1964, abin da ya ba shi matsayi a zauren wasannin ƙasar. A cewar wani saƙon da wani masoyinsa, Rudolfine Soultan ya wallafa a Facebook, Maiyegun ya rasu ne bayan ya yi fama da rashin lafiya. Soultan ya bayyana mutuwar Maiyegun a matsayin "abin baƙin ciki" kuma ya bayyana cewa suna shirin gudanar da bikin cika shekaru 17 tare cikin kwanaki biyu.…
Read More