DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da sace mahaifiyar Mawaƙi Rarara

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

Rahotanni daga Jihar Katsina sun ce Rundunar ‘Yan sandan jihar ta kama mutum biyu da ake zargin su da hannu a garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Dauda Ƙahutu Rarara, Hajiya Ibrahim.

Kakakin Rundunar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce ana cigaba da binciken waɗanda aka kama, a ƙoƙarinsu na ceto ta.

A yau juma’a ne aka yi garkuwa da Hajiyar mai kimanin shekaru 75 a ƙauyen Kahutu dake Ƙaramar Hukumar Danja, a Jihar Kastina da misalin ƙarfe 1:30 na rana.

Wannan wani huɓɓasa ne da rundunar ‘Yan sandan ta yi wajen ganin an daƙile ayyukan garkuwa da mutane da makamantansu a yankin.

By Babaji