Hasheem Abdallah ya lashe zaɓen shugabancin ASUP a BUPOLY

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Malam Hasheem Abdallah ya zama sabon Shugaban ƙungiyar Malaman Kwalejojin Kimiyya da Fasaha ta Nijeriya (ASUP), reshen Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Binyaminu Usman (BUPOLY) da ke Hadejia, bayan nasarar da ya samu a zaɓen da aka gudanar a ranar 9 ga Yuni, 2026.

Zaɓen, wanda ya gudana cikin yanayi na lumana da gasa mai ƙarfi, ya kasance ƙarƙashin sa ido na Mai Kula da Shiyyar A ta ƙungiyar ASUP, Malam Mohammed Mohammed.

Sakamakon zaɓen ya nuna cewa Hasheem Abdallah ya samu ƙuri’u 62, inda ya kayar da abokiyar takararsa, Nafisa Nasir Ma’aruf, wadda ta samu ƙuri’u 30.

Da yake jawabi bayan kammala zaɓen, Malam Mohammed Mohammed ya yaba wa mambobin reshen ƙungiyar bisa nuna dattako, haƙuri da kuma biyayya ga ƙa’idojin dimokuraɗiyya.

Ya bayyana zaɓen a matsayin ɗaya daga cikin mafi inganci, adalci da lumana da ya taɓa gani a tsawon shekarun da ya yi yana fafutuka da kuma jagoranci a cikin ƙungiyar ASUP.

A cewarsa, yadda aka gudanar da zaɓen cikin tsari da lumana ya nuna haɗin kai, balaga da kuma kyakkyawar al’adar dimokuraɗiyya da ke tsakanin mambobin reshen BUPOLY.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa cewa sabbin shugabannin da aka zaɓa za su yi aiki tukuru wajen ciyar da manufofin ƙungiyar gaba da kuma kare muradun mambobinta.

Bayan sanar da sakamakon zaɓen, Kwamitin Gudanar da Zaɓe na Reshen ƙungiyar (ELCOM) ya rantsar da sabbin shugabannin nan take domin fara aiki.

An bayyana cewa wannan sauyin shugabanci ya yi daidai da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin ASUP, musamman sashe na 8.08 da kuma dokokin gudanarwa na sashe na 14.03 da 14.04, waɗanda suka tanadi cewa zaɓaɓɓun shugabanni su karɓi ragamar aiki ba tare da tsaiko ba domin tabbatar da ɗorewar shugabanci da aiwatar da umarnin da mambobi suka ba su.

A jawabin karɓar nasara, sabon shugaban, Hasheem Abdallah, ya nuna matuƙar godiyarsa ga mambobin ƙungiyar bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya yi alƙawarin gudanar da shugabanci mai ma’ana, gaskiya da kuma haɗa kan kowa, tare da tabbatar da kare muradun mambobi da inganta walwalarsu.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta yi aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin ƙarfafa haɗin kai a cikin ƙungiyar, kare haƙƙoƙin mambobi da kuma ba da gudunmawa ga ci gaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Binyaminu Usman.

Sabon shugaban ya miƙa hannun zumunci ga dukkan mambobi, ciki har da waɗanda suka mara wa sauran ‘yan takara baya, yana mai jaddada cewa lokacin zaɓe ya wuce, kuma yanzu lokaci ne na haɗa kai domin cimma muradun ƙungiyar gaba ɗaya.

Zaɓen na nuna buɗewar sabon babi na shugabanci a ASUP reshen BUPOLY, yayin da mambobi ke fatan ganin sabon ƙwazo wajen bunƙasa ilimi, inganta walwalar ma’aikata, ci gaban cibiyar da kuma tabbatar da manufofin ƙungiyar.

By ukarofi