
1-An ayyana ranar Talata a matsayin ranar hutu a Najeriya don makokin Marigayin
2-An kafa Kwamitin Manyan Jami’an gwamnati don tsara jana’izar girmamawa ga tsohon shugaba Buhari wanda sakataren gwamnatin tarayya Sen. George Akume zai jagoranta.
3-An ɗage taron Majalisar Zartarwa ta Kasa daga gobe zuwa juma’a don zaman makoki
4 An umarci mambobi 25 na Majalisar Zartarwar da su wuce Daura don halartar jana’izar zaman makoki na kwanaki uku
4-An ayyana kwanaki 7 na zaman makoki a ilahirin Najeriya tare da yin ƙasa-ƙasa da tutar ƙasar
5- Babbar tawaga ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban kasa na can na kammala shirye-shiryen kawo gawar da iyalan mamacin gida
6- Za a yi takaitaccen faretin sojoji a filin jirgin sama na jihar Katsina don tarbar gawar.
7- Za a yi sallar jana’iza da rufe gawar a Daura.
8 An buɗe shafin karɓar ta’aziyya a dukkan ma’aikatun gwamnatin tarayya, da na hukumomi, da ilahirin ofisoshin jakadanci na Najeriya dake ƙasashen waje.
9- Ana sa ran isowar gawar Katsina da ƙarfe 12 na rana a ranar Talata.
10- Za a yi jana’izar a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025.
10- Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai karɓi gawar tsohon shugaban kasa a Katsina tare da manyan baƙi.
