Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai

A kwanakin baya ne wata Babbar Kotun Tarayya da ta ke zamanta a garin Fatakwal ta
Jihar Ribas ta samu wasu mutane biyar da laifin satar man fetur da kuma safarar man fetur ba bisa ƙa’ida ba kuma ba tare da lasisin da ya dace ba sannan ta yanke musu hukunci daban-daban.

Wannan dai na ɗaya daga cikin yawaitar satar mai da ake tafkawa a harkar mai da iskar gas wanda bisa ga dukkan alamu hakan ba wai a fannin mai kaɗai ya ke kawo cikas ba, har ma da ƙasa baki ɗaya.

Tony Elumelu, Shugaban Kamfanin Bankin UBA kuma Shugaban Kamfanin Heirs Oil and Gas, ɗaya daga cikin kamfanonin mai na Nijeriya, ya bayyana cewa, ƙasar ta yi asarar kimanin dala biliyan huɗu ga ɓarayi a watanni tara na farkon shekarar 2021.

Ya bada misali da kamfaninsa da ke haƙo ganga kusan 87,000 a rana amma a sanadiyyar ɓarayin mai yana yin asarar 50,000 daga ciki.

A nasa ra’ayin, ayyukan ɓarayin man fetur yana ɗaya daga cikin abubuwan da ke barazana ga ƙasarmu, domin kuwa akwai maƙudan kuɗaɗe a hannun mutanen da ba sa biyan haraji, kuma suna da wahala wajen daidaita shi, don haka ƙasar nan bai aminta daga gare su ba.

Haka zalika, rahoton masana’antar man fetur ta 2020 da ƙungiyar masu fafutukar tabbatar da gaskiya ta Nijeriya (NEITI) ta fitar a ranar 7 ga Maris, 2022, ya ce, a cikin shekaru biyar, 2016 zuwa 2020, ƙasar ta yi asarar sama da ganga miliyan 270 na zanyen mai ta hanyar sata da zagon ƙasa. Haka kuma, bayanai na NEITI sun nuna cewa an sace ganga miliyan 39.16 na ɗanyen mai da darajarsu ta kai dala miliyan 44.73 (Naira biliyan 15.71).

Wannan lamari ne mai matuƙar muhimmanci, musamman idan aka yi la’akari da yanayin tattalin arzikin ƙasar. Lallai abin takaici ne yadda a daidai lokacin da sauran ƙasashe masu arzikin man fetur ke murna sakamakon ƙarin farashin man, Nijeriya ba za ta iya yin haka ba saboda ayyukan waɗannan varayi da sauransu. Mafi muni har yanzu shi ne gaskiyar cewa sata yana ƙaruwa sosai kuma, bisa ga yanayin hakan na iya cigaba da ƙaruwa a cikin shekaru masu zuwa.

Sakamakon wannan lamarin, Nijeriya ba ta iya cika kasonta na ganga miliyan 1.735 a kowace rana da ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur ta OPEC ta keɓe ma ta ba. Rahoton masana’antu ya nuna cewa yawan amfanin yau da kullum a ƙasar ya kai ganga miliyan 1.417 a kowace rana tun daga watan Fabrairu.

Mummunan illolin satar mai ba wai kawai yana bayyana a cikin ɗimbin kuɗaɗen shiga da asarar da ake samu a ƙasar nan ba. Idan muka yi la’akari da abubuwan da ke haifar da gurvacewar muhalli da gurvacewar ƙasa da malalar man fetur ke haifarwa da kuma rashin tsaro da ke tasowa daga ayyukan ƙungiyoyin varayin mai a yunƙurinsu na tayar da ƙayar baya, za mu ƙara fahimtar irin ɓarnar da satar mai ta yi da kuna neman ɓarke ƙasar.

Gwamnati a matakai daban-daban na ta ƙoƙarin shawo kan matsalar ta hanyar ɗaukar matakai daban-daban. Domin a cikin babban al’amari ne da ya shafi tsaron ƙasar, ƙoƙarin da gwamnati ke yi a wannan fanni ya kasance ana hasashen jami’an tsaron ƙasar ne. A yankunan da ake samun yawaitar satar man fetur a ƙasar nan, akwai jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da jami’an tsaro daban-daban da suka wajaba domin kamo ɓarayin mai tare da gurfanar da su a gaban doka. Suna yin hakan ne tare da gwamnatocin jihohi daban-daban da hukumominsu.

Sai dai an lura cewa, duk da waɗannan matakan, lamarin satar mai na cigaba da ƙaruwa. 

Don haka akwai buƙatar gwamnatocin jihohi da na tarayya su tunkari lamarin da dukkan ƙarfi. Da farko dai, tunda akasarin ɓarayin mai da ayyukansu a cikin al’umma ne, wajibi ne hukumomi su ƙara haɗa kai da masu ruwa da tsaki a al’umma kamar sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin matasa da mata. Ya kamata saƙon ya kasance a sarari kuma babu shakka cewa duk da cewa satar mai na iya haifar da illoli na ɗan lokaci ga ’yan tsirarun da ke yin hakan, al’ummomi ne za su fuskanci sakamakon. Ana iya ƙididdige waɗannan asarar ta fuskar rushewar rayuwar jama’a, gurɓacewar muhalli da rashin tsaro.

Haka kuma gwamnati za ta iya ganowa tare da kai hari a asusun wasu sannnan ɓarayin mai tare da toshe su. Ya kamata a yi hakan tare da tallafin bankuna da cibiyoyin hada-hadar kuɗi a cikin gida da waje. Toshe kuɗaɗen da ake samu na satar mai zai zama wani tasiri ga ɓarayin mai domin ba za su iya yin almundahana da mafi yawan kuɗaɗensu ta hanyar halaltaccen tsarin banki da hada-hadar kuɗi ba.

Haka kuma akwai buƙatar a sanya sharuɗɗan aiki da wa’adin rundunonin da za su yi aiki akai-akai don yin nazari akai-akai domin ana zargin wasu daga cikinsu na haɗa baki da ɓarayin mai.

Yayin da yanayin tattalin arzikin ƙasar ke cigaba da taɓarɓarewar, yana jefa ’yan Nijeriya cikin matsanancin talauci da ƙunci, ba za mu iya bada damar ayyukan varayin man fetur su cigaba da bunƙasa a ɓangaren tattalin arzikin ƙasa ba, wanda shi ne babban hanyar samun kuɗaɗen shiga.

Satar man fetur zagon ƙasa ce ga rayuwar jama’a kuma dole ne hukumomi su ɗauki dukkan matakan da suka dace da kuma dacewa don dakatar da shi.