Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin kafa ’yan sandan jihohi

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Majalisar Wakilai ta Tarayyar Nijeriya ta amince da rahoton da ya shafi kafa rundunar ’yan sandan jihohi tare da amincewa da wasu tanade-tanaden gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya guda 18.

An cimma wannan matsaya ne a zaman majalisar da aka gudanar ranar Alhamis ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas.

Tanade-tanaden da aka amince da su na daga cikin shawarwarin da ’yan majalisar suka yi nazari a kansu yayin tattaunawar da ake yi kan gyaran Kundin Tsarin Mulki, da nufin ƙarfafa shugabanci, inganta tsaro da kuma bunƙasa aikin hukumomin gwamnati a faɗin ƙasar.

Amincewar da majalisar ta yi da rahoton kafa ’yan sandan jihohi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kira daga sassa daban-daban na ƙasar na a sake fasalin tsarin tsaro, ta hanyar bai wa jihohi damar kafa rundunonin ’yan sanda na kansu domin tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi yankuna daban-daban.

Sai dai zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Majalisar Wakilai ba ta fitar da cikakkun bayanai kan tanade-tanaden gyaran Kundin Tsarin Mulkin guda 18 da aka amince da su ba.

Ana sa ran za a bayyana ƙarin bayanai nan gaba kaɗan yayin da majalisar za ta ci gaba da bayyana sakamakon zaman nata.

By ukarofi