
Daga BELLO A. BABAJI
A ranar Litinin ne Babban Mai taimaka wa Shugaba Bola Tinubu kan Harkokin Al’umma, Aliyu Audu ya ajiye aikinsa.
A wani saƙon shafi ɗaya da ya fitar a ranar 8 ga watan Yuni, Audu ya bayyan cewa ya yi murabus, wanda hakan zai fara aiki ne a nan take.
Sannan ya yi wa Shugaban ƙasar godiya bisa ba shi damar yi wa ƙasa hidima a ƙarƙashinsa.
Ya kuma yaba wa tsohon kakakin Shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale, wanda shi ne ya bada shawara aka ba shi muƙamin a watan Agustan 2023.
Kazalika, ya yi addu’ar fatan alkhairi da cigaba da samun nasara ga gwamnatin Tinubu domin amfanin al’ummar Nijeriya.
