Sanwo-Olu ya zama Gwamnan Legas wa’adi na biyu

Daga BASHIR ISAH

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ta ayyana Babajide Sanwo-Olu a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamm wanda ya gudana a jihar ran Asabar.

Nasarar tasa ta tabbata ne bayan da ya samu ƙuri’u 762,134, inda ya doke babban abokin hamayyarsa na Jam’iyyar Labour, Gbadebo Rhodes-Vivour, wanda ya tsira da ƙuri’u 312,329, yayin da Abdul-Azeez Adediran ya zo na uku da ƙiri’u 62,449.