Sin ta himmatu wajen tabbatar da kafuwar yankin ciniki maras shinge na Asiya da Pacific

Daga CMG HAUSA

Ministan maaikatar cinikiyya ta ƙasar Sin Wang Wentao, ya ce ƙasar sa za ta yi aiki tukuru, wajen tabbatar da nasarar kafa yankin ciniki maras shinge na Asiya da Pacific, cikakke kuma bisa matsayin koli.

Minista Wang ya bayyana hakan ne cikin jawabinsa ta kafar bidiyo, yayin taro na 28 na ministocin ƙungiyar hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Pacific ko APEC, wanda ya gudana a ƙarshen mako.

Wang ya ce kamata ya yi dukkanin ƙasashe mambobin APEC su jajirce, wajen gina alumma mai makomar bai daya a matsayin tushensu, su kuma ingiza haɗin gwiwa na zahiri a sassa daban daban na cinikayya da zuba jari.

Ministan ya ƙara da cewa, ƙasar Sin za ta ƙara buɗe kofofinta tare da ci gaba da samar da matakan daidaita ci gaban tattalin arzikin duniya da na shiyyoyi.

Ya ce Sin na aiwatar da cikakkiyar yarjejeniyar haɗin kai ta raya tattalin arzikin yankin da take bisa inganci, tana kuma aiwatar da matakin gina yankin ciniki maras shinge na Asiya da Pacific mai matsayin lamba 3.0, tare da sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar ASEAN.

Bugu da ƙari, tana ci gaba da yayata amincewarta da cikakkiyar yarjejeniyar haɗin gwiwar raya tattalin arzikin zamani ta kasashen yankin Pacific.

Daga nan sai minista Wang, ya jaddada cikakken goyon bayan ƙasar Sin, ga tsarin cinikayyar sassa da dama, ƙarƙashin lemar ƙungiyar cinikayya ta duniya WTO, da tabbatar da tsaro da daidaito a fannin sarrafawa da samar da hajoji, tare da gabatar da ƙarin gajiya ga dukkanin sassa.

Fassarawa: SAMINU