Tinubu ya rantsar da Kekere-Ekun a matsayin Alƙalin Alƙalan Nijeriya ta 23

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Mai Shari’a Kudirat Olatokunbo Motonmori da aka fi sani da Kekere-Ekun a matsayin Alƙalin Alƙalan Nijeriya (CJN) ta 23 a ranar 30 ga watan Satumba, 2024, a majalisar lauyoyi da ke Fadar shugaban ƙasa a Abuja.

An haifi Kekere-Ekun ne a ranar 7 ga watan Mayu na shekarar 1958 a Landan, a ƙasar Birtaniya.

Ta yi karatun Shari’a a Jami’ar Legas inda ta samu digirin farko a shekarar 1980 wanda bayan kammala karatun makarantar shari’a ne, sai aka tabbatar da ita a matsayin lauya a ranar 10 ga watan Yuli na shekarar 1981.

Ta kuma yi digiri na biyu akan shari’a hallau a makarantar ‘London School of Economics’ da ke Landan wanda ta kammala a Nuwamban 1983.

An kuma bata muƙami a Kotun Ɗaukaka ƙara a shekarar 2004 saboda gudunmawa da take bayarwa a ɓangaren harkar ci-gaban shari’ar a Nijeriya.

A Yulin shekarar 2013 ne aka ƙara mata matsayi zuwa Mai Shari’a ta Kotun Ƙoli.

By Babaji