Zargin Rashawa: Gwamnatin Tarayya ta naɗa kwamiti don binciken hukumar gyaran hali

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Gwamnatin Tarayya ta naɗa kwamitin bincike game da batun zargin rashawa da saɓa wa ƙa’idodin aiki a Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa (NCos).

Ministan Harkokin Cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo ya ƙaddamar da kwamitin a ranar Litinin a Abuja inda ya ce kwamitin zai yi bincike game da zargin jami’an hukumar da bai wa Idris Okuneye da aka fi sani da Bobrisky mafaka.

Ministan ya ce, akwai buƙatar a tsaftace hukumar don tabbatar da gaskiya da adalci.

A kwanakin baya ne ministan wanda shine shugaban hukumar haɗaka ta hukumomin Civil Defence, gyaran hali da shige-da-fice (CDCFIB), ya dakatar da jami’ai kan saɓa wa dokokin aiki.

Ya kuma yi kira ga kwamitin su tabbatar da adalci ba tare da nuna sassauci ga kowane ɓangare ba.

By Babaji