Al’ummar ƙauyen Ohatekwe Ukawu da ke ƙaramar Hukumar Onicha a Jihar Ebonyi sun kori wani matashi mai shekaru 20, mai suna Damian Oforbuike, bayan da ake zarginsa da kashe mahaifiyarsa.
Rahotanni sun bayyana cewa matashin ya kai wa mahaifiyarsa, Onyemaechi, hari da adda, lamarin da ya jefa al’umma cikin jimami da alhini.
An ce wannan mummunan lamari ya faru ne a ƙarshen mako, inda bayan aikata laifin ya tsere zuwa cikin wani daji da ke kusa da ƙauyen.
Sai dai matasan yankin sun haɗa kai, inda suka bi sahunsa har cikin dajin, suka kama shi a wurin da yake ɓoye. Bayan kama shi, an zagaya da shi a cikin gari domin nuna abin da ya aikata, kafin daga bisani shugabannin al’umma su yanke hukuncin korarsa daga yankin tare da gargaɗin kada ya sake dawowa.
A cikin wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, an ji matashin yana amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa. Ya bayyana cewa ya kashe mahaifiyarsa ne saboda ta ƙi yi masa wanka, sannan kuma ta ƙi samar da kuɗin buɗe shago ga ɗan uwansa da ya kammala koyon sana’ar aski.
“Na kashe ta ne saboda ta ƙi yi min wanka, sannan ta ƙi taimakawa ɗan uwana da ya koyi aski ya fara sana’a,” inji shi a cikin bidiyon.
ɗan majalisar ƙaramar hukuma mai wakiltar yankin, Maduabuchi Nweke, ya tabbatar da aukuwar lamarin. Ya ce ya jagoranci matasa sama da 200 wajen shiga daji domin nemo wanda ake zargi, inda aka samu nasarar kama shi.
Ya ƙara da cewa an miƙa matashin ga rundunar ‘yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma ɗaukar matakan doka da suka dace.
Lamarin ya sake jaddada damuwa kan matsalolin tashin hankali a cikin gida, wanda ke ƙara yawaita a wasu sassan ƙasar, tare da kira ga hukumomi da al’umma su ƙara mayar da hankali kan hanyoyin magance rikice-rikicen iyali kafin su kai ga mummunan sakamako.
