Za a sallamo Osinbajo daga asibiti bayan an yi masa tiyata cikin nasara

Spread the love

Daga AMINA YUSUF ALI

An yi wa mataimaakin Shugaban ƙasar Nijeriya, Farfesa Yemi Osinbajo tiyata cikin nasara. Kuma ana sa ran za a sallame shi nan da kwanaki kaɗan bayan ya ƙara jin ƙwarin jikinsa.

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne dai aka yi wa Osinbajo tiyata a cinyarsa wanda tawagar ƙwararrun likitoci suka gudanar a wani asibiti dake yankin Ikejan Jahar Legas.

Mai taimaka wa Mataimakin Shugaban ƙasar a fanni yaɗa labarai, Laolu Akande, shi ya ba da wannan bayani a jawabin manema wanda aka wallafa a ranar Asabar.

A cikin jawabin, Akande ya bayyana cewa, wasu tawagar likitoci sun gudanar da tiyata a kan Osinbajo domin yin aiki a kan wani ciwo da ya addabe shi sakamakon wata karaya da ya tava yi a cinyarsa. Ya ƙara da cewa, amma an kammala aikin cikin nasara.

Akande ya ƙara da cewa, a halin yanzu Matakin Shugaban ƙasar yana cikin koshin lafiya da yanayi mai kyau. Kuma ana sa ran za a sallame shi daga asibiti nan da kwanaki kaɗan.

Wani rahoto da aka samu daga asibitin Duchess International Hospital dake Ikeja a jihar Legas ya bayyana cewa, tabbas su ne suka gudanar da tiyata a kan ƙashin cinyar Farfesa Osinbajo ta dama kuma tabbas aikin an yi shi, kuma an gama cikin nasara.

Har’ila yau, jawabin da asibitin ya wallafa ya bayyana cewa, a halin yanzu Farfesan yana cikin koshin lafiya kuma za a sallamo shi nan ba da daɗewa ba.

By Editor