Ƙarar da PDP ta shigar don soke cancantar Tinubu wasan yara ce – Adamu

Spread the love

Daga AMINA YUSUF ALI

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Adamu ya bayyana cewa, ƙarar da jam’iyyar PDP ta shigar don neman soke Tinubu daga takarar shugabancin ƙasar nan a 2023, da ita da wasan yara duk ɗaya ne. Domin ba wani abu ne da ya kasance barazana ga jam’iyyarsu ta APC ba.

Jam’iyyar PDP dai ta shigar da wata ƙara a kan hukumar zabe ta ƙasa INEC, da ɗan takarar APC Bola Tinubu, da Dakta Peter Obi a kan yadda suka sauya abokan takararsu na wucin gadi a yayin kuma da suke yin takara da wasu abokan takarar daban.

A cikin wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Arise TV ranar Lahadi, Adamu ya bayyana cewa, su fa dokokin wannan ƙasar fa a bayyane suke. Duk shaqiyyancin da mutum zai yi, dole akwai dokar da za ta taka masa burki.

Haka kuma a cewar sa, duk wani ɗan takara da APC ta fitar sai da ta yi zaɓen cikin gida kafin ta cimma matsayar zaɓar sa.

Adamu ya ƙara da cewa, a shari’ance APC tana da hurumin da ya ba ta damar zaɓen ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na wucin gadi wanda zai ba ta damar zaven sahihin ɗan takararta a tsanake. Kuma dokar INEC a cewar sa ita ta ba da wannan dama. “Da ba mu da wannan hurumin ma a shari’ance ma ba za mu fara ba”. A cewar sa.

Amma a cewar sa, tunda PDP sun garzaya kotu, to shi bai ma ga abin ta da jijiyar wuya a ciki ba. Sai a jira hukuncin kotu kawai. Don haka a cewar sa duk abin ba fa na ɗaga hankali ba ne.

By Editor