Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Jam’iyyar APC za ta ƙaddamar da kwamitocin tantance ’yan takarar majalisar wakilai, dattijai da na gwamnoni da ta tantance a yau da ƙarfe 12 na rana.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sulaiman Argungu ya fitar.
A cewar Argungu, za a ƙaddamar da kwamitin tantancewar ne a Fraser Suites, Abuja.
Ya kuma bayyana cewa, daga nan ne za a fara tantance masu neman kujerar gwamna, majalisar wakilai da kuma ’yan majalisar dattawa.
Argungu ya ce, za a gudanar da tantance ’yan takarar majalisar wakilai a ranar Asabar 14 ga Mayu, 2022 a otel ɗin Zeus Paradise, Abuja da ƙarfe 2 na rana.
Ya bayyana cewa, za a gudanar da tantance masu neman takarar Sanata da Gwamna a ranar 15 ga Mayu, 2022 a Fraser Suites, Abuja ranar Lahadi, da ƙarfe 10 na safe.
Jam’iyyar APC ta tsayar da ranar Juma’a 13 ga watan Mayun 2022 a matsayin ranar da za ta miƙa dukkan fom.