’Yan ta’adda sun harbe kwamandan ‘yan sanda a Katsina

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

’Yan bindiga sun harbe wani babban Kwamandan ‘yan sanda da ke kula da shiyyar Dutsinma, ACP Aminu Umar Dayi, yayin musayar wuta a ƙauyen Yoni da ke Ƙaramar Hukumar Safana a Jihar Katsina. 

Rundunar ‘yan sanda, wacce ta tabbatar da harin da aka kai wa tawagar tasu a ranar Talata, ta ce ASP Aminu Umar Dayi da wani jami’insu sun rasa ransu a rangamar. 

Kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Gambo Isah ya tabbatar wa manema labarai a Katsina, ASP Aminu Umar Dayi ya gamu da ajalisa ne a lokacin da suka je fatattakar ‘yan ta’adda. 

Ya ce sun kai ɗaukin gaggawa ne bayan sun samu rahoton ganin tawagar ‘yan bindiga sama 300 a kan mashina ɗauke da muggan makamai a dajin Zakka da ke Ƙaramar Hukumar Safana. 

Ko a ranar 18/11/2021 ma, ASP Aminu Umar ya jagoranci irin tawaga suka kai wa jama’ar garin Ɓaure a Ƙaramar Hukumar Safana ɗaukin gaggawa a lokacin da ‘yan bindiga suka kai masu farmaki. 

Bayan musayar wuta an kashe ‘yan sanda biyu; ASP Yakubu Joshua da Sajent Zaharadeen Yuguda, yayin da aka kashe ‘yan bindiga biyu, tare da ƙwace bindiga ƙirar AK-47 da harsasai masu yawa. 

Kwamishinan’yan sanda na Jihar Katsina Idrisu Dauda, ya bayyana kashe ASP Aminu Umar Daya a matsayin babban rashi a gare su, tare da shan alwashin ci gaba da fatattakar ‘yan bindiga a sassan daban-daban na jihar Katsina. 

Jihar Katsina na cikin jihohin Arewa maso Yamma da ke fama da matsalar tsaro, ko a makon nan ma sai da ‘yan bindiga suka kai hari a ƙauyen Tamawa a Ƙaramar Hukumar Kurfi, inda suka yi awon gaba da amarya da ‘yan biki, ciki har da matar ma’aikacin gidan rediyon Vision FM da ke Katsina, A’isha Ibrahim Yunusa Dutsinma. 

By Editor