Sojoji sun sake ceto wata ‘Yar Chibok mai ‘yaƴa biyu

Spread the love

Daga USMAN KAROFI a Abuja

Rundunar haɗin gwiwa a yankin Arewa maso Gabas mai suna ” Operation Haɗin Kai”, ta ceto wata ‘yar Chibok daga dajin Sambisa a Jihar Borno.

Kwamandan rundunar, Manjo Janar Waheed Shuaibu ne ya bayyana haka a lokacin da yake miƙa ta da ‘ya’yanta biyu ga gwamnatin Jihar Borno a unguwar Maimalari da ke Maiduguri, ranar Litinin.

A cewarsa, Ehi Abdul, mai shekaru 27, ta auri wani fitaccen dan ta’adda, Abu Dada a Gwoza a shekarar 2014, ya kuma tsere zuwa ƙasar Senegal.

Wani sashe na rundunar ‘Operation Haɗin Kai’ da ke dajin Sambisa ne suka ceto Ehi da ‘ya’yanta guda biyu a wani samame da suka kai.

By ukarofi