Ambaliya: Gwamnan Zamfara ya jajenta wa Borno da bada tallafin N100m

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jajenta wa gwamnatin Jihar Borno da mutanenta biyo bayan ambaliyar ruwan sama da aka yi a Maiduguri, babban birnin Borno.

Gwamna Lawal, wanda Sakataren gwamnatinsa, Malam Abubakar Nakwada ya wakiltce shi, ya jagoranci tawagar gwamnatin Zamfara zuwa gaisuwar jajen a ranar Alhamis.

Kakakin gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya ce dalilin ziyarar shi ne don a jajenta wa gwamnatin Borno da mutanen jihar kan ambaliyar wacce ta auku a makon da ya gabata, kamar yadda ya faɗa a cikin wani saƙo da ya fitar.

A lokacin da ya ke gabatar da jawabi yayin ziyarar Malam Nakwada ya sanar da cewa, gwamnatin Zamfara ta bada tallafin Naira miliyan 100 ga Borno don a raba wa mutanen da lamarin ya rutsa da su da kuma ƙarfafa alaƙar taimakon juna a tsakanin gwamnatocin biyu.

Ya kuma bayyana takaici ganin yadda ambaliyar ta raba sama da mutane miliyan ɗaya da matsugunansu, ya na mai fatan kar irin hakan ya sake faruwa a nan gaba.

By Babaji