Gwamnati ba ta biya buƙatunmu ba – ASUU ta sake barazanar yajin aiki

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta fitar da wata sabuwar barazanar yajin aiki inda ta zargi Gwamnatin Tarayya da ƙin biyan duk wasu buƙatu da ta nema duk kuwa da tabbacin da ta yi na warware saɓanin da ke tsakaninsu na tsawon shekaru.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce baya ga tawagar da aka kafa kwanan nan domin tattaunawa da ASUU, babu wata ƙwaƙƙwarar yarjejeniya da aka cimma.

Osodeke ya ce tun daga lokacin ne ƙungiyar ta kammala nata ɓangaren na tattaunawa da ƙungiyar, inda take jiran martani daga wakilan gwamnati. “Yau watanni biyu ke nan, kuma tawagar gwamnati ba ta dawo wurinmu ba, balle a sanya hannu kan wata sabuwar yarjejeniya. Ma’anar wannan ci gaban shi ne, ‘yan siyasa ba su damu da jami’o’in gwamnati ba,” inji shi.

Ya zargi gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu da yin sakaci a ɓangaren ilimi na manyan makarantu, yana mai cewa gwamnatocin da suka shuɗe a zahiri sun yi ƙoƙari ta fuskar jin daɗin malamai.

“Babu wata matsala da wannan gwamnati ta warware ta dindindin tun lokacin da ta hau mulki, don haka, a matsayinmu na ƙungiya muna da ƙwarin gwiwar cewa babu abin da ya canza.

“Har yanzu muna ba da wannan tsohon labari ne, yayin da masu hannu da shuni sukan tura yaransu zuwa ƙasashen waje don yin karatu su dawo daga baya su ɗauki muƙaman da ake kira masu kuɗi, musamman a cibiyoyin gwamnati, suna barin yara marasa galihu da wahala.”

Osodeke ya ce dole ne wannan labari ya canza idan Nijeriya na son samun ci gaba na gaske a matsayin ƙasa. Sai dai ya bayyana cewa ‘yan ƙungiyar ASUU za su gana nan ba da jimawa ba domin yanke shawara kan matakin da za su ɗauka na gaba.

A halin da ake ciki, ƙungiyar ɗaliban Jami’o’i ta ƙasa (NAUS), ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta riƙa hada-hadar shugabannin ASUU, a wani ɓangare na ƙoƙarin daƙile yajin aikin da ake yi da kuma kawo cikas ga shirye-shiryen ilimi.

Shugaban ƙungiyar, Josiah Oche, ya yi alƙawarin ci gaba da fafutukar ganin an inganta kuɗaɗe na jami’o’i, da inganta rayuwa, da samar da ingantattun kayan aikin koyo da koyarwa ga ɗalibai.

“Wannan ya haɗa da yunƙurin samar da ingantattun kayan aiki, ɗakunan karatu na zamani, da masauki mai araha ga kowa.”

By ukarofi