Rashin tsaro: Shugaban DSS ya gana da Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa

Spread the love

Darakta Janar na hukumar ƴan sandan farin kaya (DSS) Adeola Ajayi, ya kai wa Shugaban Ƙasa Bola Tnubu rahoton halin da ake ciki game da sace-sacen ɗalibai da ƴan bindiga bindiga suka yi a jihohin Kebbi da Neja da ke arewacin ƙasar.

A sanarwar da Bayo Onanuga, Kakakin Shugaban ƙasa ya fitar, shugaban na DSS ya gana da Tinubu ne a jiya Juma’a da dare.

A ranar Litinin ne ƴan bindiga suka sace ɗalibai mata 25 daga wata makarantar sakandare ta mata a garin Maga da ke ƙaramar hukumar Danko-Wasagu a jihar Kebbi.

Sai kuma ranar Juma’a, inda aka yi awon-gaba da ɗalibai fiye da 300 da malamansu a wata sakandaren da ke Papiri a cikin Jihar Neja.

Tuni Tinnubu ya soke balaguronsa zuwa taron G20 a Afirka ta Kudu saboda halin matsalar tsaron, kuma ya tura Ministan Tsaro Abubakar Badaru Neja, yayin da Ƙaramin Ministan Tsaro Bello Matawalle ya tafi Kebbi domin shawo kan al’amuran.

By Babaji