Fannin kare haƙƙin ɗan-Adam na buƙatar jajirtattun mutane – MƊD

Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya jaddada ƙa’ida cewa, “an haifi kowani ɗan Adam da ‘yanci kuma suna da mutunci da haƙƙi.”

Guterres ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa don cika shekaru 75 da ƙaddamar da yarjejeniyar kula da haƙƙoƙin bil’adama na duniya a ranar 10 ga Disamba 2023.

Ya ce, “Yarjejeniyar Haƙƙin ɗan-Adam ta Duniya tana da mahimmanci a yau kamar yadda take a lokacin da aka amince da ita shekaru 75 da suka gabata.

“Yarjejeniyar duniya taswirar hanya ce, tana taimaka wa kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe da haɓaka rayuwar zaman lafiya da mutunci ga duka al’umma”.

Bugu da ƙari, Guterres ya sake bayyana damuwarsa kan yadda duniya ke kauce wa wannan tafarki, inda tashe-tashen hankula talauci, yunwa da rashin daidaituwa ke ƙara ta’azzara.

“Yayin da muke aiki don sabunta tsarin duniya da kuma sa su zama masu tasiri a wannan ƙarni na 21st, dole ne ‘yancin ɗan adam ya kasance yana da matsayi na musamman kuma na tsakiya.

“Ina kira ga ƙasashen mambobin ƙungiyar da su yi amfani da wannan bikin cika shekaru 75, da kuma taron koli na gaba a shekara mai zuwa, don ƙarfafa himmarsu kan kimar da ba ta dace ba.

“Kuma a ranar kare haƙƙin bil’adama, ina kira ga mutane a duniya da su inganta da mutunta ‘yancin ɗan adam, a kowace rana, ga kowa da kowa, a ko’ina,” in ji Guterres.