Daga BASHIR ISAH
Bayanai da MANHAJA ta samu na nuni da cewa wani tsohon dan majalisar wakilai daga Jihar Delta ya mutu a wajen kallon wasan kwallon da aka buga tsakanin Super Eagles da Afrika ta Kudu na gasar AFCON 2023 a ranar Laraba.
Wata majiya ta kusa da ahalin marigayin ta ce, Ojuogboh ya yanke jiki ya fadi ne a lokacin da aka bai wa Afirka ta Kudu damar buga fenariti a kurarren lokaci a yayin wasan da aka buga a filin Stade de la Paix da ke Bouake.
A halin rayuwarwa, marigayi Cairo Ojuogboh tsohon dan Majalisar Wakilai ne daga jam’iyyar APC wanda ya wakilci Mazabar Ika a Jihar Delta.
Haka nan, ya taba rike mukamin Babban Daraktan Hukumar Bunkasa Yankin Niger Delta (NDDC).