Editor

9513 Posts
An samu raguwar mace-mace ta dalilin AIDS da kashi 70 – MƊD

An samu raguwar mace-mace ta dalilin AIDS da kashi 70 – MƊD

Daga BASHIR ISAH Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa, an samu raguwar mace-mace sakamakon cutar kanjamau (AIDS) da kashi 70 a faɗin duniya tun 2004. Majalisar ta ce duk da wannan matsayi da aka cimma, har yau AIDS na kashe mutum guda a cikin duk minti guda. Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres ne ya bayyana haka cikin saƙon da ya fitar albarkacin Ranar Yaƙi da AIDS ta Duniya ta 2023. António Guterres ya ce, "ya zama wajibi mu ga bayan AIDS a matsayin ƙalubale ga lafiyar al'ummar duniya ya zuwa 2030." Ya ƙara da cewa, domin kawar da…
Read More
Yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta kammala shirin yaƙi da cin zarafin mata a Nijeriya

Yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta kammala shirin yaƙi da cin zarafin mata a Nijeriya

Daga WAKILINMU Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya tare da haɗin gwaiar Tarayyar Turai da sauran takwarorinsu sun kamala wani shirin yaƙi da cin zarafin mata a Nijeriya mai laƙabin ‘spotlight initiative’ tare da mika ragamar cibiyoyin gudanar da aikin ga gwamnatin Nijeriya. An kamala shirin ne a otel na Transcorp da ke Abuja a tsakiyar makon nan inda wasu ministoci da shugabannin hukumomin gwamnati suka halarta. A jawaban da suka gudanar daban-daban, Babban Jami’in Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Mattias Schmale da Wakiliyar Tarayyar Turai a Nijeriya da ECOWAS, Samuela Isopi sun ce shirin ya samu nasara bisa yadda yake bai…
Read More
Ɗumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet

Ɗumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet

Daga WAKILINMU Hukumar ta bayyana hakan ne a wajen wani taron kara wa juna sani da ta shirya wa ‘yan jarida tare da haɗin gwiwar Majalisar Ɗinkin Duniya na, wajen tunatar da ‘yan jarida kan dumamar yanayi ta yadda za su faɗakar da al’ummar ƙasar nan. Taron ya gudana ne a Otel din Rock Biew da ke Abuja, inda ta ce wannan wani sharar fage ne kan babban taron da aka fara a ƙasar Dubai daga ranar 30 ga Nuwamba zuwa 12 ga Disamba. Hukumar NiMet ta yi nemi ‘yan jarida su kara kaimin fadakar da al’ummar Nijeriya kan illar…
Read More
Babu wanda ya saci kuɗi a Nijeriya kamar Diezeni – TY Ɗanjuma

Babu wanda ya saci kuɗi a Nijeriya kamar Diezeni – TY Ɗanjuma

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon babban hafsan sojin ƙasa, Theophilus Ɗanjuma, ya yi zargin cewa tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison-Madueke ta yi fice wajen cin hanci da rashawa. Ɗanjuma ya ce Alison-Madueke ita ce mace ɗaya tilo a Nijeriya da ya sani da ta yi fice wajen cin hanci da rashawa. Ya yi magana ne a lokacin da yake ƙaddamar da cibiyar lafiya ta Goodwill Medical Center (GMC) a Umuchigbo, Iji Nike a ƙaramar hukumar Enugu ta Gabas, ranar Talata. A cewar tsohon hafsan sojojin, Diezani ta kafa tarihin da har yanzu babu wanda ya buge ta.…
Read More
Za mu yi bincike kan takardun hukuncin zaven gwamnan Kano – NJC

Za mu yi bincike kan takardun hukuncin zaven gwamnan Kano – NJC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Ƙoli Kan Harkokin Shari'a ta Nijeriya (NJC) ta ce za ta gudanar da bincike kan batutuwan da suka shafi takardun hukuncin zaɓen gwamnan Kano da kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta yi. Jaridar Daily Trust ta ambato wasu jami'an majalisar shari'ar ƙasar, na bayyana haka a lokacin da suka ziyarci ofishinta da ke Abuja. An dai samu ruɗani kan takardun hukuncin shari'ar da kotun ɗaukaka ƙarar ta yi ranar 17 ga watan Nuwamba a shari'a tsakanin gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, da Nasiru Yusuf Gawuna na APC. A hukuncin da kotun…
Read More
NDLEA ta kama ton 15.7 na haramtattun ƙwayoyi a Kano

NDLEA ta kama ton 15.7 na haramtattun ƙwayoyi a Kano

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar NDLEA reshen jihar Kano a ranar Litini ta ƙona tan 15.7 na haramtattun ƙwayoyi da ta kama a jihar. Shugaban hukumar Buba Marwa ya ce dakarun hukumar da jami’an tsaron tashar jiragen saman Malam Aminu Kano MAKIA suka kama haramtattun ƙwayoyin tsakanin watan Oktoba 2020 zuwa Oktoba 2023. Marwa wanda Shugaban fannin gudanar da bincike na hukumar Samuel Bashir-Gadzama ya wakilta ya ce hukumar ta ƙona waɗannan muggan ƙwayoyi domin daƙile yaɗuwarsu cikin al’umma. Shugaban hukumar na jihar Kano Abubakar Idris-Ahmad ya ce daga cikin tan 15,193.365 da aka ƙona akwai kilogiram 9,824.098…
Read More
Bambancin marubutan onlayin da mawallafa littattafai a bayyane yake – Milhart

Bambancin marubutan onlayin da mawallafa littattafai a bayyane yake – Milhart

"Ban yi wa marubuta adalci ba, idan na ce suna da girman kai" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Fadeela Yakubu matashiyar marubuciyar onlayin ce daga Jihar Gombe, wacce za a iya kiranta da ƴar baiwa, saboda yadda take da basira da hikimar yin abubuwa da dama a fagen ƙirƙira, domin ilimantar da matasa, faɗakarwa da kuma nishaɗantarwa. Bayan kasancewarta marubuciya, Fadeela, wacce ake kira da Milhart, sananniya ce a manhajar Tiktok da YouTube, inda take wallafa kalaman soyayya da faɗakarwa, da kuma karanta littattafan Hausa. Allah Ya yi mata baiwa ta zaƙin murya ta yadda take amfani wannan baiwar da Allah…
Read More
Mu nemi aure a wajen surukai nagari

Mu nemi aure a wajen surukai nagari

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU A duk lokacin da wani batu ya tashi kan matsalar auratayya, wani Hadisi ne yake yawan faɗo min a rai. Mattanin Hadisin na cewa, Ma'aikin Allah Mai Tsira da Aminci ya cewa sahabbansa, 'Ku kiyayi ciyar da dabbobinku da ciyawar da ta fito a kan juji.' Sai sahabbai suka tambaye shi abin da yake nufi da haka, sai Manzon Allah (SAWA) ya ƙara da cewa, 'Ku guji aurar da ’ya’yanku ga dangin da basu da kyakkyawar shaida, masu munanan halaye.' Saƙon da za mu ɗauka daga wannan Hadisi shi ne cewa, idan za mu yi…
Read More
Gwamna Lawal ya sha alwashin ganin bayan ‘yan fashin daji a Zamfara

Gwamna Lawal ya sha alwashin ganin bayan ‘yan fashin daji a Zamfara

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya sha alwashin kawo ƙarshen 'yan fashin dajin da suka addabi jihar. Ya bayyana haka ne a ranar Laraba sa'ilin da ya ziyarci sansanin bai wa Dakarun Rundunar Kare Alumma (CPG) inda suke karɓar horo, shirin da gwamnatin jihar ta ƙirƙiro domin daƙile 'yan fashin daji a faɗin jihar ta Zamfara. Cikin sanarwar da ya sanya wa hannu wadda MANHAJA ta samu kwafi, Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya ce horon da dakarun ke ci gaba da karɓa ya ƙara wa jihar da ma al'ummarta ƙwarin gwiwa dangane da sha'anin yaƙin…
Read More
Duk matar da ba za ta yi sana’a ba ba ta san kanta ba – Fa’iza Badawa

Duk matar da ba za ta yi sana’a ba ba ta san kanta ba – Fa’iza Badawa

"Rashin amincewa mace ta yi sana'a da mijinta zai yi ne kawai matsalar ta a kasuwanci" Daga MUKHTAR YAKUBU A yanzu da yanayin rayuwa ya sauya, a kullum a na ta kiraye-kirayen mata da su kama sana'a ko wani kasuwanci wanda za su dogara da kansu, musamman ma dai a gidagen zaman aurensu, duba da cewa, a wannan zamani da muke ciki ko mazan na shan kashi a hannun taɓarɓarewar tattalin arzikin ƙasa, ta yadda matsin rayuwa sai ta’azzara yake yi. Hakan na daga dalilan da ya sa maza da yawa samunsu ya ragu, don haka hidimtawa iyali sai ya…
Read More