Editor

9513 Posts
Nguru: ya kamata mu san Annabi ya faku……

Nguru: ya kamata mu san Annabi ya faku……

Daga IBRAHIM GARBA NAYAYA Nguru gururun duniya! Wannan yana daga cikin kirarin da muka taso muka ji ana yi wa wannan gari namu ma’abocin ɗaukaka da daraja! Gari, wanda ya samar da manyan mutane, shin malamai ne ko ‘yan kasuwa ne, ko wasu manyan ma’aikatan gwamnati! Gari, wanda ya yi shuhura da zaman lafiya da son addini da son masu addini! Gari, wanda mazaunansa suka taso suke ganin kowa ɗan’uwan juna ne! Gari, wanda a baya za ka iske mazaunansa na bibiyar matsalolin juna domin su magance musu ba don su yayata ba! Gari, wanda mutum guda zai ɗauki nauyin…
Read More
‘Yan sanda sun hallaka shugabannin ‘yan bindiga a Katsina

‘Yan sanda sun hallaka shugabannin ‘yan bindiga a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar 'yan sanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewar ta samu nasarar kashe wasu manyan shugabannin 'yan bindiga uku da su ka addabi al'umar jihar. Daga cikin waɗanda aka kashe akwai ƙasurgumin ɗan bindiga Bala wuta wanda ya addabi ƙaramar hukumar Jibiya, sauran su ne Dogo na Sahura da kuma Hassan Bukuru. Bayanin haka na ƙunshe cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar, ASP Abubakar Aliyu ya fitar ranar Laraba a Katsina. Ya ce, arangamar ta faru ranar 25 ga watan Nuwamba,2023 da misalin ƙarfe 10:30 na safe lokacin da su ke gudanar da sintirin haɗin…
Read More
Yadda ma’aurata za su cigaba da raya soyayyarsu bayan aure (1)

Yadda ma’aurata za su cigaba da raya soyayyarsu bayan aure (1)

Tare da AMINA YUSUF ALI Barkanmu da sake haɗuwa a wannan jaridar taku mai farin jini ta Blueprint Manhaja. Yau za mu tattatuna a game da abubuwan da maaurata za su yi don cigaba da raya soyayyarsu ko da bayan an yi aure. Abinda uka sani ne, kuma ba ɓoyayyen abu ba ne soyayya takan mutu murus bayan aure. Akwai dalilai da yawa da sukan sa hakan ta faru. Wannan ya sa a wannna mako muke tafe da waraka a kan wannan laura da ta kan gallabi kusan kowanne aure. Shi ne ni kuma na yi linqaya a kogin zamantakewa…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe ‘yan sanda biyu a Imo

‘Yan bindiga sun kashe ‘yan sanda biyu a Imo

Daga BASHIR ISAH Aƙalla mutum uku ciki har da 'yan sanda biyu sun mutu sakamakon sabon harin da 'yan bindiga suka kai a yankin Ƙaramar Hukumar Ahiazu Mbaise, Jihar Imo. Rahotanni sun ce, harin ya auku ne a ranar Litinin, 27 ga Nuwamban 2023, inda ɓata-garin suka buɗe wa 'yan sandan wuta wanda a nan take suka hallaka jami'ai biyu da wani mutum guda. Majiyarmu ta ce harin ya auku ne a lokacin da sabon Kwamishin 'Yan Sandan Jihar, Danjuma Aboki, ya kai ziyarar aiki a yankin Mbaise domin ƙara wa jami'ansu ƙwarin gwiwa. Mai magana da yawun rundunar 'yan…
Read More
Babban Hafsan Tsaro ya buƙaci ƙarin tallafi ga fannin tsaro

Babban Hafsan Tsaro ya buƙaci ƙarin tallafi ga fannin tsaro

*Sojoji sun kammala atisayen "Operation Mugun Bugu" Daga BASHIR ISAH Babban Hafsan Tsaro na Nijeriya, Janar Christopher Musa, ya yi kira da a ƙara tallafin da ake bai fannin tsaro musamman ɓangaren mayaƙan sama domin ci gaba da ƙarfafa musu game da yaƙi da matsalar tsaro. Kiran na zuwa ne a lokacin da Rundunar Sojin Nijeriya ke kammala atisayen “Operation Mugun Bugu" na makonni wanda shi ne irinsa na biyu da ta shirya a 2023. Yayin atisayen wanda ya gudana a garin Kontagora, Jihar Neja, dakarun sun yi gwajin makamai tare da ɗaukar sabbin dabarun aiki. Da yake jawabi ta…
Read More
Yadda mutuwar Daraktan Kannywood, Aminu S.Bono ta girgiza al’umma 

Yadda mutuwar Daraktan Kannywood, Aminu S.Bono ta girgiza al’umma 

*Gwamnan Kano ya girgiza da mutuwar Aminu S. Bono, inji Abba El-Mustapha*Rasuwar Bono ta haifar da wagegen giɓi a Kannywood – Ganduje*Zan biya ma sa bashin da ke kansa, cewar jaruma Aisha Humaira*Jaruma Rashida Maisa’a ta ɗauki nauyin karatun ɗan marigayin*Furodusa Kufaina ya yafe bashin da yake bin Bono Daga AISHA ASAS  Duk da cewa, mutuwa rigar kowa ce kuma mun amince duk mai rai sai ya ɗanɗani zafin mutuwa, hakan bai hana mu alhini da jimami yayin da muka rasa wani masoyinmu ba. Duk da kasancewar mutuwa abar tayar da hankali ce a kodayaushe, kuma babu ta yadda za…
Read More
Wane ne Adolf Hitler?

Wane ne Adolf Hitler?

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haifi Adolf Hitler ranar 20 ga watan Afirilu na shekara 1889, ya kashe kansa ranar 30 ga watan Afirilu na shekara 1945 bayan an ci Jamus da yaƙi. An aifi Adolf Hitler ranar 20 ga watan Afrilu na shekara 1889 wato shekaru 122 kenan da suka gabata. An aife shi a wani gari mai suna Braunau-am Inn, a ƙasar Austriya kusa da iyakar ƙasar da Jamus. Shi ne na huɗu a gidansu. Mahaifinsa wani jami'in Custum ne, ya rasu a yayin da Hitler ke da shekaru 14 da aihuwa. Marubuta tarihin Hilter sun ce bai…
Read More
NARTO suna ƙoƙarin wajen wayar da kan direbobi – Muhammad Inuwa

NARTO suna ƙoƙarin wajen wayar da kan direbobi – Muhammad Inuwa

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Alhaji Muhammad Inuwa Sakataren Ƙungiyar Masu Motocin Sufuri na Ƙasa, rashen Jihar Kano ya bayyana cewa, ƙungiyar su ta NARTO na taka muhimmiyar rawa wajen ganin ma'aikatan su sun bi duk kanin ƙa'idojin tuqi da kuma kula da lafiyar ababan hawan su a koda yaushe domin ganin an rage munanan haɗurran da akan samu akan hanyoyinmu na Nijiriya musamman a watanni huɗu ƙarshen kowacce Shekara. Kamar dai yadda sakataren ƙungiyar NARTO na Kano ya bayyana a lokacin taron wata ƙungiya mai suna MAMA da ta shirya don wayar da kan masu tuƙa ababan hawa da…
Read More
Gwamnan Kano ya naɗa sabon Shugaban Ma’aikatan Jihar

Gwamnan Kano ya naɗa sabon Shugaban Ma’aikatan Jihar

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Alhaji Abdullahi Musa a matsayin sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar. Hakan dai na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya aiko wa Manhaja, Inda ya ce naɗin na zuwa ne bayan da tsohon shugaban ma’aikatan jihar Kano, Usman Bala ya kammala aikinsa, inda ya yi ritaya daga aikin gwamnati tun a watan Mayun shekara ta 2023, kamar yadda doka ta tanada . Sanarwar ta ce Alhaji Abdullahi Musa ƙwararen ma’aikacin gwamnati ne da…
Read More
Sai an tallafa wa ƙananan masana’antu idan ana son karya farashin shinkafar gida – Ambasada Ali

Sai an tallafa wa ƙananan masana’antu idan ana son karya farashin shinkafar gida – Ambasada Ali

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Ambasada Alhaji Ali Idris Mai Unguwa Kura, Shugaban Ƙungiyar Masu Sarrafa Shinkafa, Sayarwa da Noma ta na Ƙaramar Hukumar Kura, kuma Shugaban Ƙungiyar Masu Ƙananan Masana'antu da Matsakaita na Sarrafa Shinkafa na Ƙasa, reshan Jihar Kano, ya bayyana cewa ƙorafi da koke-koke da ake yi na tsadar shinkafa, wannan ya samo asali ne daga ƙarancin masu sarafa ta. Alhaji Ali ya ƙara da cewa, "idan har ana son noma shinkafa ya bunƙasa cikin tsafta, ya kuma wadata, da babu tsakuwa ko ƙuƙus, a cikin ta cikin farashi mai sauƙi da rahusa, sai an tallafawa ƙanana…
Read More