27
Nov
Daga BASHIR ISAH Babban Alƙalin Najeriya (CJN), Mai Shari'a Olukayode Ariwoola, ya jaddada cewa cece-kucen da ake yi a ƙasa ba zai canja hukunce-hukuncensu kan shari'un siyasa ba. Kawo yanzu, hukunce-hukuncen da Kotun Ƙoli ta yanke kan batutuwan zaɓe, wanda hakan ya yi sanadiyar soke nasarar wasu gwamnoni da 'yan majalisu, ya haifar da zazzafar muhawara a tsakanin 'yan ƙasa musamman 'yan siyasa. Da yake jawabi a wajen buɗe zama na musamman na fannin shari'a na 2023/2024 da kuma rantsar da sabbin manyan lauyoyin Nijeriya su 58, Ariwoola ya buƙaci alƙalai da su yi tsayin daka game da ayyukansu. Ya…
