Editor

9513 Posts
Yan sanda sun kama mutane takwas da ake zargi da ƙona motar rundunar a Katsina

Yan sanda sun kama mutane takwas da ake zargi da ƙona motar rundunar a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar 'Yan Sanda a Jihar Katsina, ta bayyana cewa ta kama mutane takwas da take zargi bisa ƙona motar jami'anta masu kula da zirga-zirgar ababen hawa a titunan jihar. Lamarin dai ya faru ne a titin Ƙofar Guga ɗaya daga cikin manyan hanyoyi a babban birnin jihar da aka fi samun cinkoson ababen hawa. Rahotanni sun bayyana cewa rikici ya ɓarke tsakanin jami'an rundunar (MTD) da kuma masu ababen hawa dake amfani da hanyar. 'Yan sandan sun yi ƙoƙarin kama wani mai babur da ya karya dokar tuƙi, sai dai wasu mutane dake kan titin…
Read More
Babu Nijeriya a cikin ƙasashen Afirka 12 da suka samu allurar rigakafin Maleriya karon farko

Babu Nijeriya a cikin ƙasashen Afirka 12 da suka samu allurar rigakafin Maleriya karon farko

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An cire Nijeriya daga cikin jerin ƙasashen Afirka 12 da aka shirya ba su allurai miliyan 18 na maganin Zazzaɓin Cizon Sauro na farko. Ƙungiyar Gavi, da Ƙungiyar Allurar Rigakafi, da Hukumar Lafiya ta Duniya, da Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ne suka bayyana hakan a wata sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar a ranar Laraba. Shugaban WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus ya shaida wa wani taron manema labarai cewa, "Maleriya na ɗaya daga cikin cututtukan da suka fi kashe mutane a Afirka, inda ke kashe yara kusan rabin miliyan 'yan ƙasa…
Read More
Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Shugaba guda huɗu da rage harajin kiran waya da kashi biyar cikin 100

Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Shugaba guda huɗu da rage harajin kiran waya da kashi biyar cikin 100

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya sa hannu a kan umarnin shugaba guda huɗu, da nufin rage wasu nau'o'in haraje-haraje ga al'ummar ƙasar. Ɗaya daga cikin umarnin shugaban ƙasar shi ne dakatar da harajin kashi biyar a kan ayyukan wayoyin sadarwa da kuma dakatar da harajin da aka tsawwala a kan kayan da ake sarrafawa a cikin gida. Mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan ayyuka na musamman da al'amuran sadarwa, Dele Alake ya faɗa ranar Alhamis cewa shugaban ƙasar ya kuma sa hannu a kan Dokar Kuɗi ta 2023, wadda a yanzu ta jingine…
Read More
Ba za mu iya aiwatar da ƙarin kaso 40 na kuɗin lantarki ba – PHEDC

Ba za mu iya aiwatar da ƙarin kaso 40 na kuɗin lantarki ba – PHEDC

Daga AMINA YUSUF ALI  Kamfanin rarraba hasken lantarki na garin Fatakwal (PHEDC) ya bayyana cewa, sam ba zai iya ƙarin kuɗin lantarki zuwa kaso 40% ba a dai-dai wannna lokaci.   Kamfanin ya ƙara da cewa, a yanzu haka sun samu nasarar yi wa kaso 57 na masu amfani da wutar mitoci, amma fa a cewar su har yanzu guda 285,000 daga cikinsu ba su da mitoci.  Manajan Daraktan kuma babban jami'in zartarwar  PHEDC, Dakta Benson Uwheru, shi ya bayyana haka a garin Fatakwal a ranar Larabar da ta gabata a yayin taron 'yan jarida na ranar bikin cika shekara guda…
Read More
Tinubu bai fitar da jerin sunayen ministoci ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Tinubu bai fitar da jerin sunayen ministoci ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Alhamis Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa, ba a kammala shirya jerin sunayen ministocin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai naɗa ba. Mataimakin Musamman ga Shugaban Ƙasa kan ayyuka na musamman, sadarwa da dabaru, Dele Alake, ne ya bayyana haka a yayin ganawa da manema labarai a fadar gwamnati da ke Abuja. Alake ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da jita-jitar da ke tattare da jerin sunayen ministocin da ake jira. "Game da jerin ministocin, babu gaskiya a cikin duk waɗannan abubuwan," inji Alake. "Lokacin da Shugaban Ƙasa ya natsu…
Read More
Ba zan wahalar da ’yan Nijeriya kamar gwamnatin Buhari ba – Tinubu

Ba zan wahalar da ’yan Nijeriya kamar gwamnatin Buhari ba – Tinubu

*Ya rage harajin da aka ƙaƙaba na shigo da motoci da sauransu  Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sauya wasu harajin da aka sanya a cikin mintunan ƙarshe da tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rattava wa hannu, yana mai cewa ba zai shaƙe ‘yan Nijeriya ya wahalar da su kamar yadda gwamnatin baya ta yi ba. Shugaban ya soke harajin ne a cikin umarnin zartarwa a jiya Alhamis, 6 ga Yuli, 2023. Harajin sun haɗa da dakatar da harajin kashi 5 da ake cece-kuce kan ayyukan sadarwa; Harajin Kore na kashi 10…
Read More
Tinubu zai tsayar da ranar ƙidaya a Nijeriya – Shugaban hukumar

Tinubu zai tsayar da ranar ƙidaya a Nijeriya – Shugaban hukumar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Hukumar Ƙidaya ta Ƙasa (NPC), Nasir Isa Kwarra, ya bayyana cewa, Shugaba Bola Tinubu zai bayyana sabbin ranakun da Nijeriya za ta gudanar da ƙidayar jama'a da kuma gidaje. Shugaban NPC ya shaidawa manema labarai a ranar Alhamis bayan ganawarsa da shugaban ƙasar cewa ci gaba da gudanar da ƙidayar jama’a zai haifar da ƙarin kuɗaɗe. Kidayar da gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta tsara tun daga ranar 3 zuwa 7 ga watan Mayun 2023 an ɗage shi zuwa ranar da gwamnatin Tinubu ta tantance. Bayan ganawa da shugaban ƙasar a ranar Alhamis, Kwarra…
Read More
Kotu ta bayar da belin Abba Kyari bayan wata 18 a tsare

Kotu ta bayar da belin Abba Kyari bayan wata 18 a tsare

Daga MAHDI M. MUH’D Mai shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ya bayar da belin tsohon shugaban ɓangaren ’yan sanda masu kai ɗaukin gaugawa (SARS), Malam Abba Kyari, bayan ya shafe watanni 18 a tsare. Kotun ta ce an bayar da belin ne kasancewar, dakataccen jami'in ɗan sandan bai tsere daga gidan yarin Kuje ba a lokacin da aka kai hari gidan yarin a ranar 5 ga Yuli, 2022. Mai shari’a Omotosho ya bayyana cewa, yadda Kyari da tawagarsa suka ƙi tserewa a lokacin da aka kai wa gidan yarin hari, inda kusan kashi 90 cikin…
Read More
Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

An yi hasashen cewa 'yan Nijeriya miliyan 25 na iya fuskantar matsananciyar yunwa tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2023 (lokacin bazara) idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba don magance matsalar. Mutane dai na ganin cewa, tsadar man fetur ne babban ummul kaba'sin tsadar abinci da ake fama da ita a Nijeriya, wanda hakan zai saka al'ummma da dama cikin matsananciyar yunwa. Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nakalto Cadre Harmonise a watan Oktoba na shekarar 2022, wani bincike na abinci mai gina jiki ƙarƙashin jagorancin gwamnati da Majalisar Ɗinkin Duniya, yana mai nuni da…
Read More
INEC ta shigar da ƙarar kwamishinanta na Adamawa, Hudu Ari, a kotu

INEC ta shigar da ƙarar kwamishinanta na Adamawa, Hudu Ari, a kotu

Daga MAHDI M. MUH’D Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Nijeriya (INEC) ta shigar da tuhume-tuhume shida a gaban kotun sauraron ƙararrakin zaɓe, kan dakataccen kwamishinan zaɓe na Jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari. Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar mai ɗauke da sannun shugaban sashen wayar da kan al'umma na hukumar, Festus Okoye, ta ce an shigar da ƙarar ce a babbar kotun jiha da ke Yola, a Jihar Adamawa. Sanarwar ta kuma tabbatar da samun takardar kammala bincike kan laifukan da suka shafi zaɓe daga hannun ’yan sanda, bayan kammala bincike kan laifukan zaɓe da aka yi a babban…
Read More