Editor

9513 Posts
Hamayya da neman karɓe kujerata ta Sanata ɗimuwa ce kawai – Rufa’i Hanga

Hamayya da neman karɓe kujerata ta Sanata ɗimuwa ce kawai – Rufa’i Hanga

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Sanata Rufa'i Sani Hanga ya bayyana cewa masu hamayya akan kujerarsa ta Sanatan Kano ta Tsakiya "in ba su yi hamayya ba, ba su yi halasci ba domin dama abinda ita siyasa ta gada kenan abinda rayuwa ta gada kenan." Ya bayyana haka ne da yake zantawa da 'yan jarida a Kano, inda ya ce ba yadda za ka yi da ɗan hamayya mutum dole ko waye kai dole ka samu maƙiya da masoya, sai dai kullum fata shine masoya su fi maƙiya yawa. Ya ce shi baya jin ciwon hamayya ko abinda ake faɗa…
Read More
Ɗan takarar Gwamna ya je Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da shaidu 8,000

Ɗan takarar Gwamna ya je Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da shaidu 8,000

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutumin da ya yi wa Jam’iyyar PDP takara a zaɓen Gwamnan Jihar Ogun na 2023, Ladi Adebutu, a ranar Talata ya isa kotun sauraron kararrakin zaɓen jihar da shaidu har guda 8,000. Ɗan takarar dai na ƙalubalantar nasarar da Dapo Abiodun ya samu a zaɓen Gwamnan Jihar da aka gudanar ranar 18 ga watan Maris ɗin da ya gabata. A kwafin ƙarar tasa mai lamba EPT/OG/GOV/03/2023, ɗan takarar ya ce ya shigar da ƙarar ce saboda yana zargin ba a bi Dokar Zaɓe ta Nijeriya ba a yayin zaɓen. Alqalai uku ne dai suke…
Read More
Masarautar Zazzau ta dakatar da Hakimi kan zargin lakaɗa wa matashi duka

Masarautar Zazzau ta dakatar da Hakimi kan zargin lakaɗa wa matashi duka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Masarautar Zazzau ta dakatar da Alhaji Mustapha Adamu Ubaidullah daga kujerarsa ta Marafan Yamman Zazzau. Masarautar ta ce ɗaukar matakin ya biyo bayan koken da al’ummar Unguwar Magajiya da ke birnin Zariya suka miƙa, na zargin cin zarafin wani mutum da ake yi wa basaraken. A takardar sanarwar da mai magana da yawunta, Abdullahi Aliyu Ƙwarbai ya fitar ranar Talata, masarautar ta ce ta amince cikin gaggawa ta dakatar da Hakimin har sai abin da hali ya yi a nan gaba. Shi dai Alhaji Mustapha, majalisar ta same shi ne da laifin zartar…
Read More
Burundi ta bijire wa Majalisar Ɗinkin Duniya

Burundi ta bijire wa Majalisar Ɗinkin Duniya

Ƙungiyoyin fararen hula sun koka da matakin da gwamnatin Burundi ta ɗauka na ficewa daga zauren zaman nazartar kundinta na take haƙƙoƙin bil’adama da Majalisar Ɗinkin Duniya ke jagoranta. Wannan ɗabi’ar da Burundi ta nuna ta jefa fargaba a zukatan ƙungiyoyin fararen hula da suka nuna damuwa kan yadda ƙasashen duniya ke bijire wa Majalisar Ɗinkin Duniya. Lokaci zuwa lokaci, Majalisar Ɗinkin Duniya na gudanar da nazari kan yadda gwamnatocin ƙasashe ke mutunta dokokin kare haƙƙin bil’adama. Sai dai a wani yanayi na ba-zata, tawagar wakilai 15 ta Burundi ta fice daga zaman da ta yi tare da Kwamitin Kare…
Read More
A karon farko an naɗa mace Alƙalin-alƙalai a tarihin Kano

A karon farko an naɗa mace Alƙalin-alƙalai a tarihin Kano

Daga BASHIR ISAH A ranar Alhamis da ta gabata Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tabbatar da naɗin Dije Aboki a matsayin Alƙalin-Alƙalan Jihar Kano. Wannan naɗi ya zama al'amari na tarihi a jihar, kasancewar Dije ce mace ta farko da za ta riƙe wannan matsayi a jihar ta Kano. Naɗin nata ya biyo bayan wasiƙar da Gwamna Abba Yusuf ya aike wa majalisar jihar wadda aka gabatar da ita a zauren majalisar a ranar Alhamis. Shugaban Majalisar, Ismail Falgore, shi ne ya karanto wasiƙar yayin zaman majalisar a ranar Alhamis da ta gabata. Da fari, an naɗa Dije Muƙaddashin Alƙalin-alƙalan…
Read More
Bankun sun canza ƙa’idar cirar kuɗi a ATM zuwa Naira 200,000

Bankun sun canza ƙa’idar cirar kuɗi a ATM zuwa Naira 200,000

Daga AMINA YUSUF ALI Watanni da dama bayan da bankuna sun ƙayyade adadin kuɗin da za a iya cira a ATM a rana guda, yanzu sun ƙara adadin zuwa Naira 200,000. A yanzu haka za a iya cire har Naira 200,000 a kowacce rana a na'urar ATM ɗin daga asusun mutum guda.  A jiya ne dai Bankin Zenith ya sanar wa masu ajiyarsa ta hanyar saƙon imel cewa, yanzu za su iya cire kuɗi daga asusunsu har Naira Naira 200,000 a kwacce rana daga na'urar ATM ɗin bankin a faxin ƙasar nan, ba tare da la'akari da bankin da aka…
Read More
Amarya ta yi ajalin angonta a Bauchi

Amarya ta yi ajalin angonta a Bauchi

Wata amarya mai suna Maimuna Suleiman 'yar shekaru 21, ta kashe mijinta Aliyu Muhammad ta hanyar daɓa masa wuƙa a unguwar Ƙofar Ɗumi dake Bauchi. 'Yan sandan yankin sun tabbatar da aukuwar hakan tare da cewa, suna tsare da amaryar don zurfafa bincike. Mai magana da yawun 'yan sanda na Bauchi, ASP Aminu Gimba Ahmed ya ce lamarin ya faru ne ranar 5 ga Yulin 2023 da misalin ƙarfe 6:00 na yamma. Ya ƙara da cewa, bayan da suka samu labari sun garzaya gidan inda suka ɗauki mijin da matar zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa (ABUTH). Ya…
Read More
Bankin Nijeriya ya samar da ma’aikacin mutum-mutumi a bankin

Bankin Nijeriya ya samar da ma’aikacin mutum-mutumi a bankin

Daga AMINA YUSUF ALI  Bankin FirstBank na Nijeriya ya ƙaddamar da wani mutum-mutumin ma'aikacin banki a reshensa na  Adetokunbo Ademola VI, (DXC) a Legas don kula da koken masu ajiyar bankin.  Folake Ani-Mumuney, Shugaban rukunin bankuna, da kasuwanci da hulɗar kamfanoni na FirstBank, shi ya bayyana haka a cikin wani jawabi da gabatar a ranar Alhamis ɗin makon da ya gabata.  A cikin jawabin nasa ya bayyana cewa, mutum-mutumin yana da girkakkiyar kyamara ta bidiyo da fasahar na'ura mai ƙwaƙwalwa wanda zai mayar da shi tamkar ɗaya daga cikin ma'aikata masu fara'a na reshen bankin.  Wannan wani yunquri ne irinsa…
Read More
Ancelotti zai koma horar da ’yan wasan Brazil

Ancelotti zai koma horar da ’yan wasan Brazil

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Real Madrid, Carlo Ancelotti zai karɓi ragamar horar da Tawagar Ƙwallon Ƙafar Brazil a kaka mai zuwa kamar yadda shugaban hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar, Ednaldo Rodrigues ya bayyana. Brazil wadda ta lashe kofin duniya har sau biyar, na da kwarin guiwar cewa, Ancelotti, shi ne zai jagoranci ƙasar zuwa gasar Copa America da za ta gudana a cikin watan Yunin 2024. Brazil ba ta da wani tsayayyen koci tun lokacin da aka kammala gasar kofin duniya a bara, bayan da kocinta Tite ya yi murabus jim kaɗan da aka lallasa a hannun Croatia. Ancelotti zai…
Read More
Sarkin Rano yana bada kulawa sosai wajen kare kimar al’adun mu – Uban Doman Rano

Sarkin Rano yana bada kulawa sosai wajen kare kimar al’adun mu – Uban Doman Rano

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana cewa Sarkin Rano, Alhaji Kabiru Autan Bawo da cewa yana kan gaba wajen himmatuwa da bada kulawa wajen ɗabbaƙa raya al'adun mu na gargajiya. Mataimakin Sufeto Janar na 'Yan sanda mai kula da sashen sufuri, Yusuf Usman Chiromawa. Uban Doman Rano. Walin Garun Malam shine ya bayyana hakan da yake zantawa da 'yan jarida. Ya ce koda shiga ta Ado da Autan Bawo Sarkin Rano yake a koyaushe yana wakiltar suturar al'dummu na gargajiya ne, duk wani abu na cigaba yana ƙoƙari ya ga ya tafi da tsari na al'adarmu don kiyaye kimar…
Read More