Editor

9513 Posts
Zaɓar Asma’u Inuwa a matsayin Shugabar Matan Gwamnonin Arewa sara ne kan gaɓa – Esther Amisu

Zaɓar Asma’u Inuwa a matsayin Shugabar Matan Gwamnonin Arewa sara ne kan gaɓa – Esther Amisu

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Esther Amisu, 'yar siyasa ce a jihar Gombe kuma ƙwararriya a ɓangaren sanin harkokin siyasa, ta ce ba shakka matan Gwamnonin Arewa ba su yi zaɓen tumun dare ba na zaɓar Hajiya Asma'u Muhammad Inuwa Yahaya, uwargidan gwamnan Gombe a matsayin jagora. Esther Amisu, ta ce zaɓar Asma'u Inuwa Yahaya da matan gwamnonin suka yi zai ƙara bai wa mata dama na shiga harkokin siyasa domin Asma'u mace ce da a kullum take ƙoƙarin mata sun samu kulawa ta musamman an kuma basu wani kaso mai tsoka a muqaman siyasa. Ta yi wannan batu…
Read More
Raɗɗa ya saka hannu kan yarjejeniya da UNDP don inganta tsaro a Jihar Katsina

Raɗɗa ya saka hannu kan yarjejeniya da UNDP don inganta tsaro a Jihar Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya saka hannu a kan yarjejeniyar fahimtar juna da Hukumar Raya Ƙasa ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNDP don ƙaddamar da cibiyar bayar da kariya a Arewa maso Yammacin Nijeriya. Taron mai ɗumbin tarihi ya gudana ne a ɗakin taro na Majalisar Ɗinkin Duniya dake Abuja. Cibiyar samar da tsaro yankin Arewa maso yamma shiri ne na hukumar UNDP Nijeriya. Ma’aikatar harkokin waje da ofishin jakadancin Norway ne ke ɗaukar nauyin shirin dake da nufin tallafa wa jihohin Sakkwato, Zamfara, da Katsina. Shirin na neman yin amfani da matakan…
Read More
Buhari bai hana Shugaba Tinubu binciken jami’an gwamnatinsa ba – Garba Shehu

Buhari bai hana Shugaba Tinubu binciken jami’an gwamnatinsa ba – Garba Shehu

Daga UMAR GARBA a Katsina Kakakin tsohon shugaban ƙasa Malam Garba Shehu ya bayyana cewa tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, bai hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu binciken jami’an gwamnatinsa ba. Malam Garba Shehu ya bayyana haka ne cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Tiwita inda ya kuma musanta cewa tsohon Shugaban ƙasar yana katsalandan a binciken da sabuwar gwamnati ke son yi kan jami’an gwamnatin da ta gabata. “Idan za a yarda da abin da aka ce a soshiyal midiya, tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari yana buƙatar mutumin da ya gaje shi, Shugaba Bola Ahmed Tinubu kada…
Read More
Alhazan Zamfara na hanyar komowa gida

Alhazan Zamfara na hanyar komowa gida

Daga BASHIR ISAH A wannan Alhamis alhazan Jihar Zamfara na hanyarsu ta komowa gida bayan kammala Hajjin 2023. Bayanan Hukumar Aikin Hajji ta Nijeriya (NAHCON), sun nuna jirgin sama na kamfanin FLYNAS mai lamba XY7954 ya baro Jidda zuwa Sakkwato ɗauke da alhazan Jihar Zamfara 383 da kuma wasu jami'ai biyu. NAHCON ta ce jirgin ya baro Jidda ne da misalin ƙarfe 12:23 na rana. Da wannan, hukumar ta ce baki ɗaya adadin alhazan Nijeriya da aka yi nasarar dawo da su gida tun bayan kammala Hajjin na bana, ya kama mutum 3,427 a tsakanin sawun jirgi 9.
Read More
Gobara ta kashe mutum biyu a Nijar

Gobara ta kashe mutum biyu a Nijar

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga ƙasar Nijar mai maƙwabtaka da Nijeriya sun ce, mutum biyu sun mutu yayin da wasu sun jikkata sakamakon gobarar da ta tashi a kamfanin SONIDEP da ke birnin Zinder. Rahotanni na nuni da cewa, iftila'in ya faru ne a ranar Labara a wani wurin ajiyar man fetur na kamfanin da lamarin ya shafa. Haka nan, an ce gobarar ta ƙone wasu motocin dakon man fetur biyu ƙurmus. A cewar majiyarmu, gobarar ta tashi ne a daidai lokacin da motocin dakon man suke ƙoƙarin sauke mai a ma'ajin man kamfanin na SONIDEP. Ta ce gobarar ta…
Read More
Cire tallafin mai: Gwamnan Taraba ya rage kuɗin makaranta da kashi 50

Cire tallafin mai: Gwamnan Taraba ya rage kuɗin makaranta da kashi 50

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ba da sanarwar rage kuɗin makaranta na jami'ar jihar da kashi 50% domin rage wa 'yan jihar raɗaɗin tallafin man da aka cire. Mai magana da yawun Gwamnan, Emmanuel Bello ne ya bayyana haka a Jami'ar Jihar Taraba, inda ya ce batun ilimi na daga fannonin da gwamnatin jihar ta bai wa fifiko. Ya ce tuni Gwamna Kefas ya ayyana dokar ta ɓaci a fannin ilimin jihar domin bunƙasa shi. Majiyarmu ta ce galibin ɗaliban jami'ar sun nuna jin daɗinsu da wannan mataki da Gwamnan ya ɗauka, inda suka ce hakan…
Read More
Mutum 16 sun mutu sakamakon shaƙar iskar gas a Afirka ta Kudu

Mutum 16 sun mutu sakamakon shaƙar iskar gas a Afirka ta Kudu

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Afirka ta Kudu sun ce, wasu mutum 16 sun mutu sakamakon shaƙar iskar gas. An danganta lamarin wanda ya auku a ranar Laraba a Boksburg da ke gabashin Johannesburg, da yoyon tukunyar gas a yankin. Bayanai sun nuna an samu yoyon tukunyar gas ɗin ne sakamako haramtattun ayyukan masu haƙar zinari a yankin. Jami'an yankin sun ce waɗanda lamarin ya shafa sun haɗa da mata da ƙananan yara. Kazalika, sun ce samfurin gas ɗin da ya yi wannan ta'asar, wato 'Nitrate oxide gas', galibi da shi masu haƙar ma'adinai ta haramtacciyar hanya ke amfani…
Read More
Likitoci sun fara yajin aikin gargaɗi a Nasarawa

Likitoci sun fara yajin aikin gargaɗi a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Likitoci ta Nijeriya (NMA) reshen Jihar Nasarawa, ta fara yajin aikin gargaɗi na kwana biyar bayan da gwamnati ta gaza wajen cim ma buƙatun mambobinta. Shugaban NMA a jihar, Mr. Peter Attah, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai ranar Laraba a garin Lafia, babban birnin jihar. Ya ce sun yanke shawarar tafiya yajin aikin ne a wajen taron da ƙungiyar ta shirya a ranar Talata. Yana mai cewa, gwamnati ta gaza wajen cim ma buƙatunsu a cikin wa'adin kwanaki 21 da ƙungiyar ta ƙayyade mata farawa daga ranar 13 ga Yuni, 2023. Ya ƙara…
Read More
Zan gyara hanyar Kontagora-Tagina, Tagina-Minna – Gwamna Bago

Zan gyara hanyar Kontagora-Tagina, Tagina-Minna – Gwamna Bago

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Neja Muhammad Umar Bago, ya ba da tabbacin fara aikin gyaran hanyar Kontagora zuwa Tagina, Tagina zuwa Minna. Bago ya ba da wannan tabbacin ne sa'ilin da ya kai wa Sarkin Sudan na Kontagora, Alh. Muhammad Barau Mu'azu II, ziyarar goron sallah a masarautar Kontagora, a ranar Laraba. A cewarsa, hanyar Kontagora zuwa Tagina, Tagina zuwa Minna na buƙatar kulawa matuƙa don bai wa jama'a damar yin zirga-zirga cikin aminci da kuma kiyaye aukuwar haɗurra. Hanyoyin da lamarin ya shafa hanyoyi ne masu muhimmanci wanda sun daɗe da lalacewa amma na su samu kulawar gwamnatin…
Read More
Gwamnan Kano ya naɗa Hisham Habib shugaban Radio Kano

Gwamnan Kano ya naɗa Hisham Habib shugaban Radio Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanar da naɗin Hisham Habib, shugaban ƙungiyar 'yan jaridu ta yanar gizo reshen Jihar Kano, a matsayin Manajan Daraktan Gidan Rediyon Kano. Naɗin wanda ya fara aiki nan take, na cikin wata sanarwa da Hisham ɗin ya fitar, wanda kuma ke riƙe da muƙamin muƙaddashin mai magana da yawun gwamna Abba Kabir Yusuf. Hisham Habib gogaggen ɗan jarida ne, wanda ya yi digirinsa na farko a fannin Turanci a Jami’ar Bayero Kano, sannan ya yi digiri na biyu a fannin koyon aikin jarida. Kafin wannan naɗin, Hisham ya…
Read More