05
Jul
Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga sun kashe wani lauya mai suna Barista Ahmad Muhammad Abubakar a Jihar Zamfara. Majiyarmu ta ce 'yan bindigar sun bi margayin ne har gidansa da ke garin Kwatarkwashi, cikin Ƙaramar Hukumar Bungudu suka hallaka shi. Kafin rasuwarsa, marigayi Muhammad shi ne sakataren walwala na Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya reshen Gusau. Kazalika, shi ne ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Zamfara a mazaɓar Bunguɗu ta Yamma ƙarƙashin Jam'iyyar NNPP a yayin babban zaɓen da ya gabata. Duk da dai Rundunar 'Yan Sandan Zamfara ba ta ce komai kan batun ba, sai dai majiya ta kusa da marigayin…
