Babaji

4782 Posts

Gwamnatin Tarayya ta soke tsarin JSS da SSS a sakandare kan yawan yaran da ba sa zuwa makaranta

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta umarci a yi wa tsarin ilimin Nijeriya garambawul, sakamakon rahoton da ke nuna cewa kusan ɗalibai miliyan 20 sun fice daga makaranta. Ministan Ilimin, Dakta Tunji Alausa ne ya sanar da haka yayin ƙaddamar da Kwamitin Ministoci na Aiwatarwa da Sanya ido na Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC) a Abuja. Ya ce, tsarin raba raba makarantar sakandare ƙarama, wato Junior Secondary School (JSS) da Senior Secondary School (SSS) ya gaza samar da mafita ga yawan ɗaliban da ba sa zuwa makaranta. A madadin haka, ya ce za a samar da wani tsari…
Read More

Sojoji sun ceto ɗalibai 10 sa’o’i bayan Boko Haram ta farmaki makaranta a Borno

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun tsaron Nijeriya sun yi nasarar ceto ɗalibai guda 10 da aka yi garkuwa da su a makarantar sakandare ta Lassa da ke Ƙaramar Hukumar Askira-Uba a Jihar Borno sa'o'i bayan da 'yan ta'adda suka farmaki makarantar yayin da ake tsaka da rubuta jarrabawar NECO a ranar Litinin. Rahotanni sun bayyana cewa, maharan sun je makarantar ne a akan babura, inda suka yi garkuwa da ɗaliban kana daga bisani dakarun Atisayen Haɗin Kai suka ƙaddamar da atisayen bincike da ceto ta taimakon jiragen sama na yaƙi. A wata sanarwa da jami'in yaɗa labaran sojoji…
Read More

Kano: Samar da jari ne ginshiƙin bunƙasa kasuwanci, inji Shugaban ‘yan kasuwa a Bichi

Ƙungiyar 'Yan kasuwar Zamani ta Bichi Traders Multi-Purpose Cooperative Society Limited, ta yi kira ga gwamnati, shugabanni, masu ruwa da tsaki, manyan 'yan kasuwa da masu zuba jari da su haɗa hannu wajen bunƙasa harkokin kasuwanci a Ƙaramar Hukumar Bichi. Shugaban Ƙungiyar 'Yan kasuwar Zamani ta Bichin, Alhaji Abubakar Mazahimu Sale ne ya bayyana wannan kiran, bayan kammala gina kasuwar Kabiru Abubakar Ultra-Modern Market Bichi, ƙarkashin jagorancin Ɗanmajalisar Tarayya mai wakiltar Bichi, Alhaji Abubakar Kabir Abubakar. Ya ce, a wannan karon da ake shirin fara amfani da rukuni na biyu na shagunan da aka kammala, lokaci ne da yakamata shugabanni…
Read More

Shugaban Paraguay ta bada hutu bayan ƙasar ta doke Jamus a gasar Kofin Duniya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Santiago Pena na Paraguay ya ayyana ranar Talata, 30 ga Yuni a matsayin hutu ga 'yan ƙasarsa bayan da ta doke Jamus a zagayen 'yan 32 a wasan gasar Kofin Duniya da ke gudana a Nahiyar Amurka. Paraguay ta samu nasarar hayewa zuwa zagaye na gaba ne bayan nasara da 4 da 3 a bugun fenarati bayan Kai Havertz ya farke ƙwallon da Julio Enciso ya zura wa Jamus. Wannan sakamako ya sa a karon farko a tarihi 'yan wasa maza na Jamus sun rasa nasara a zangon bugun fenarati a gasar Kofin…
Read More

Kofin Duniya: Moroko za ta kara da Kanada bayan cire Holland a zagayen ‘yan 32

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Moroko ta doke ɗaya daga cikin ƙasashen ake hasashen ka iya lashe gasar Kofin Duniya da fari, wato Netherlands bayan an tashi 3 da 2 a zangon bugun da kai sai mai tsaron gida a wasan da aka gudanar a tsakaninsu. Hakan ya biyo bayan tashi a wasan 1 da 1, bayan shafe mintina 120 ana gumurzu a filin wasa, lamarin da ya ba wa ƙasar Afirkan nasarar tsallakewa zuwa zagayen 'yan 16. Ɗan wasa Cody Gakpo ne ya fara zura ƙwallo a ragar Moroko a lokacin da aka kai minti na 72,…
Read More

El-Rufa’i zai ci gaba da zama a hannun ICPC yayin da kotu ta yi watsi da buƙatar beli

Babbar Kotun Jihar Kaduna ta ƙi amincewa da buƙatar beli da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya gabatar, inda ta umarci cewa zai ci gaba da kasancewa a hannun Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) har sai an cigaba da shari'ar. A hukuncin da Mai Shari'a Dirisu Khobo ya yanke a ranar Litinin, ya bayyana cewa El-Rufai bai gabatar da hujjoji masu gamsarwa da za su sa kotu ta yi amfani da ikon ta wajen ba shi beli ba. Kotun ta kuma ce babu wasu dalilai na musamman da suka cancanci a sake shi kafin kammala shari'ar.…
Read More

2027: INEC ta ba APC, PDP ADC, NDC da wasu jam’iyyu damar ɗora sunayen ‘yan takararsu a shafinta

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, ta ba jam'iyyar APC da wasu jam'iyyun siyasa lambobin damar shiga tsarin ɗora sunayen 'yan takara a shafinta na yanar gizo domin shirye-shiryen babban zaɓen 2027. Rahotanni sun bayyana cewa, jam'iyyun da suka samu damar sun haɗa da APC, PDP, ADC, da kuma NDC da wasu jam'iyyu da nufin ba su damar gabatar da sunayen 'yan takararsu a tsarin na INEC cikin wa'adin da hukumar ta gindaya. Bayan kammala ɗora sunayen, 'yan takarar za su fafata ne domin neman kujerun a shugaban ƙasa, Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai da kuma…
Read More

Kofin Duniya: Martinelli ya tura Brazil zuwa zagayen ‘yan 16 bayan zura ƙwallo a minti na 95

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gabriel Martinelli ya zura ƙwallo a raga a minti na 95, wanda hakan ya ba Brazil nasarar doke Japan da ci 2 da 1 a wasansu na zagayen 'yan 32 na gasar Kofin Duniya da ke cigaba da gudana a Nahiyar Amurka. Wannan al'amari ya sa Japan ta rasa damar tsallakewa zuwa zagaye na gaba duk da cewa ita ta fara zura ƙwallo a ragar Brazil a zangon farko na wasan ta ɗan wasa Kaishu Sano. Bayan minti goma da fara zangon na biyu ne ɗan wasa Casemiro ya farke wa Brazil a lokacin…
Read More

Gwamnatin Tarayya ta amince da jagorancin farar hula a NYSC yayin sabbin sauye-sauye a hukumar

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta amince da aiwatar da manyan sauye-sauye a Hukumar kula da matasa masu yi wa ƙasa hidima (NYSC), da nufin inganta tsarin gudanar da shirye-shiryenta da kuma daidaita su da buƙatun zamani. Ministan Ci-gaban Matasa, Mista Ayodele Olawande ne ya bayyana haka ga manema labarai, jim-kaɗan bayan ganawa da Shugaba Bola Tinubu a zaman majalisar zartarwa a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, ranar Litinin. Daga cikin sauye-sauyen da aka amince da su akwai maye gurbin tsarin jagorancin sojoji da na farar hula a hukumar, tare da sake fasalin kayan aikin masu…
Read More

Boko Haram sun sace ɗalibai bayan halaka malami ana tsaka da rubuta jarrabawar NECO a Borno

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Borno ta tura jami'ai zuwa ƙauyen Lassa da ke Ƙaramar Hukumar Askira-Uba bayan satar wasu ɗalibai da ba a tantance da adadinsu ba yayin da ake tsaka da rubuta jarrabawar NECO daga wasu da ake zargin 'yan ta'adda ne. Maharan, waɗanda ake kyautata zaton mayaƙan Boko Haram ne sun farmaki makarantar ne da misalin ƙarfe 9 na safe, inda suka riƙa harbe-harbe na kan-mai-uwa-da-wabi kana daga bisani suka yi awon-gaba da ɗalibai da matan da ke sayar da kayan abinci a farfajiyar makarantar, kamar yadda binciken farko ya nuna.…
Read More