Babaji

4782 Posts

Sojoji sun cafke ɗan tsegumin ISWAP yayin shirin hare-hare a sansanonin sojoji a Borno

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun tsaro na Atisayen Haɗin Kai a Arewa maso Gabas, sun yi nasarar kama wani da ake zargin ɗan tsegumi ne ga ƙungiyar ISWAP bisa zargin wani shiri na kai farmaki ga sansanin sojoji guda biyu a Jihar Borno. Rahotanni sun bayyana cewa, Muhammad Shuaibu ne sunan wanda ake zargin, wanda dakarun Bataliya ta 212 da ke sansanin ayyuka (FOB) na yankin Chabbol suoa yi ram da shi bayan samun wani bayanin sirri akan shirin ƙaddamar da farmakin. Wata majiyar sojoji ta shaida wa manema labarai cewa, an kama Shuaibu ne yayin wani sintiri…
Read More

Yadda ‘yan bindiga suka haska maƙudan kuɗaɗen fansar da suka karɓa a wani bidiyo

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yadda wasu 'yan bindiga suke nuna wasu maƙudan kuɗaɗe da ake zargin na fansa ne da suka karɓa a hannun jama’a sakamakon garkuwa da makusantansu, lamarin da ya haifar da damuwa akan ƙamarin rashin tsaro a Nijeriya. Sanannen ɗan jarida, Bakatsine, wanda ya shahara da ruwaito labaran rikici da rashin tsaro ne ya wallafa bidiyon a ranar Asabar. Ɗan jaridar, wanda ya wallafa bidiyon ta kafar X, ya ce: "wannan bidiyon ya nuna 'yan bindiga na baje kolin kuɗaɗen da aka samu…
Read More

ISIS ta fitar da bidiyon babban rumbun makaman sojoji da ta ƙwace a Nijar

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta da ƙungiyar ISIS ta wallafa bayan wani mummunan hari a sansanin sojojin Jamhuriyar Nijar a yankin Inates, inda aka nuna wani babban rumbum makaman sojoji da aka ƙwace yayin samamen. A ranar Lahadi ne ɗan jarida da ya shahara wajen yaɗa labaran ayyukan 'yan ta'adda, Bakatsine, ya wallafa bidiyon da ke nuna manyan makaman daga rumbun sojin. Saidai a yayin haɗa wannan rahoto, ba a kai ga tabbatar da sahihancin bidiyon ba da kuma adadin makaman da aka haska. A cewar ɗan jaridar, al'amarin ya…
Read More

NDC ta zargi INEC da hana ta shiga shafin wallafa sunayen ‘yan takararta

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Jam'iyyar adawa ta NDC ta zargi Hukumar Zaɓe ta Ƙasa da yin watsi da buƙatarta ta samun damar shiga shafin yanar gizo hukumar da za ta wallafa sunayen 'yan takararta. Haka kuma, jam'iyyar na shirin shigar da ƙarar ƙalubalantar hukuncin kotu na soek rajistarta. Wannan ci-gaba na zuwa ne a daidai lokacin da wata Babbar Kotun Tarayya ta umarci INEC ta soke rajistar NDC, hukuncin da ya jefa jam'iyyar cikin halin rashin tabbas akan sahihancin shigarta zaɓukan da ke tafe. Sakataren yaɗa labaran NDC, Osa Director ya ce NDC ta buƙaci INEC da ta…
Read More

Sakkwato: ‘Yan bindiga sun halaka limami da wasu uku, sun sace mutum 12 a wani sabon hari

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun halaka wani limami tare da wasu mutum uku a wani hari da suka kai a ƙauyen Illela Dawagware da ke ƙaramar hukumar Goronyo ta Jihar Sakkwato. Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 12:20 na daren ranar Lahadi inda suka riƙa harbe-harbe, lamarin da ya yi sanadin mutuwar Limamin mai suna Mallam Liman Lawwali Na Audu a gidansa da kuma wasu mutum uku. Baya ga waɗanda aka kashe, maharan sun kuma yi garkuwa da mazauna ƙauyen mutum 12 tare da tafiya…
Read More

An shirya taron tunawa da Buhari bayan shekara ɗaya da rasuwarsa babu yayatawa a Abuja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Za a gudanar da taron tunawa a Abuja a ranar Litinin, 13 ga watan Yuli, 2026, domin karrama marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar 13 ga Yulin 2025. Ana sa ran abokai, makusanta da masu fatan alheri su haɗu a babban birnin tarayyar domin yin addu'o'i da kuma tunawa da karamcinsa, kamar yadda rahotanni suka bayyana. An shirya wannan taro ne da nufin tunawa da hidimar da marigayin ya yi wa ƙasa, jagoranci da gudunmawarsa ga Nijeriya, bayan da aka yi masa jana'iza a mahaifarsa Daura ta Jihar Katsina…
Read More

Kofin Duniya: An kammala haɗa wasannin ‘yan 32 yayin da ƙasashen Afirka tara suka shiga karo na farko a tarihi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An kammala shirya jaddawalin ƙasashen da za su fafata a zagayen 'yan 32 na gasar Kofin Duniya na 2026 da ke cigaba da gudan a Nahiyar Amurka bayan da aka kammala wasannin zangon rukunin-rukuni. NBC Sports ta ruwaito cewa, za a gudanar da wasannin zangon ne cikin kwanaki shida a jere, a wani salo na musamman da ya bambanta da fasalin baya. A yau ne za a fara wasannin a birnin Los Angeles inda mai masaukin baƙi, Kanada, za ta kara da Afirka ta Kudu. Ga jaddawalin wasannin kamar yadda jaridar IntelRegion ta wallafa:…
Read More

Filato: Dilolin makamai sun amsa sayar wa ‘yan ta’adda bisa farashi mai tsoka

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana cewa, waɗanda aka kama da hannu a laifin gudanar da haramtattun masana'antun haɗa makamai a Jihar Filato, sun amsa cewa suna samarwa tare da sayer wa 'yan ta'addan Fulani saboda suna biyan farashi mai tsoka akan sauran masu siya, fallasa abin da hukumomi suka kira da babban sababin ruruwar rikicin jihar. Selong Sule, shugaban dakarun Atisayen Safe Haven (OPSH) a lokacin da yake ganawa da taron manema labaran sojoji a Jos a madadin Babban jami'in rundunar (GOC) ta uku kuma kwamandan atisayen ne ya bayyana haka. A cewar Zagazola…
Read More

Da dama sun jikkata yayin da sabbin kuratan sojoji suka yi hatsari a hanyar Zariya

Wasu daga cikin sababbin matasan da aka ɗiba aikin soja sun yi hatsari yayin da suka taho daga Jihar Imo domin fara karɓar horo a sansanin horar da Sojojin Nijeriya da ke Zariya, Jihar Kaduna, a safiyar Asabar. A cewar wasu majiyoyin soji, masu neman aikin na kan hanyarsu ta zuwa cibiyar horaswa domin fara horon soja lokacin da hatsarin ya faru. An ce tafiyar tana ƙarƙashin kulawar Laftanar Kanal P.D. Ngal. Majiyar ta ce sun tashi daga Jihar Imo zuwa Zariya kafin wannan mummunan hatsari ya afku. Bidiyoyin da ke yawo a kafafen sada zumunta sun nuna wasu daga…
Read More

Kofin Duniya: Portugal, Croatia, Ghana, Aljeriya, Austriya da Ingila sun tsallake zuwa zagayen ‘yan 32 yayin da Messi da Kongo suka kafa tarihi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An kammala wasannin rukunin K da L a gasar Kofin Duniya na 2026 da ke gudana a Amurka cikin wani salo mai kama da wasan kwaikwayo a ƙoƙarin zuwa zagayen 'yan 32. A sakamakon haka ne Portugal za ta kara da Croatia a Toronto a ranar 2 ga Yuli, a wata karanbatta da ka iya zama wasa na ƙarshe a gasar ga Cristiano Ronaldo mai shekaru 41 ko kuma Luka Modric. Portugal ta koma matsayi na biyu ne bayan da ta tashi wasa babu ci tsakaninta da Kolombiya a rukunin K, yayin da Croatia…
Read More