02
Jul
Babbar Kotun Tarayya a Abuja, ta tabbatar da halaccin shugabancin tsagin su Sanata David Mark a jam'iyyar ADC da kuma yin watsi da ƙarar ɗan Majalisar Wakilai, Leke Abejide ta ƙalubalantar naɗin Mark da Rauf Aregbesola a matsayin shugaba da sakataren jam'iyyar na ƙasa. Mai shari'a Musa Liman ya ce kotun ba ta da hurumin shiga harkokin cikin gida na jam'iyya, sannan ya bayyana cewa Abejide bai nuna cewa an tauye masa wata doka ko haƙƙi ba, kuma bai fara amfani da hanyoyin sasanta rikici na cikin jam'iyyar ba kafin ya garzaya kotu. Kotun ta kuma yanke cewa miƙa shugabancin…
