Babaji

4782 Posts

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta jingine hukuncin kotun Oyo na barin ɗalibai mata sanya hijabi a UI International School

Kotun Ɗaukaka Ƙara a Ibadan ta jingine hukuncin Babbar Kotun Jihar Oyo da ya ba ɗalibai mata Musulmai damar sanya hijabi a makarantar International School da ke ƙarƙashin Jami'ar Ibadan. A hukuncin da aka yanke ranar Juma’a, kotun ta bayyana cewa makarantar makaranta ce mai zaman kanta, don haka tana da ikon tsara dokokinta na tufafi da tsarin ɗabi’a ba tare da katsalandan ba. Wannan hukunci ya biyo bayan ƙarar da wasu iyaye Musulmai suka shigar suna neman a ba ’ya’yansu damar sanya hijabi a makarantar, suna mai cewa hakan wani ɓangare ne na ’yancin addininsu. Tun farko, babbar kotun…
Read More

INEC ta ƙara sati biyu don ci gaba da yi wa kaɗa ƙuri’a rajista

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, ta sanar da ƙarin wa'adin rajistar masu kaɗa ƙuri'a (CVR) da mako biyu domin ba wa ƙarin 'yan Nijeriya damar yin rajista gabanin babban zaɓen 2027. A cewar hukumar, matakin ya biyo bayan buƙatun da jama'a da ƙungiyoyi suka gabatar na neman a ƙara lokaci, saboda yawan mutanen da har yanzu ba su samu damar yin rajista ba. Hakan na nufin masu shekaru 18 da haihuwa ko sama da haka, da kuma waɗanda ke son sabuntawa ko sauya bayanansu, za su cigaba da samun damar yin rajista cikin sabon…
Read More

Tsohon sakataren gwamnatin Benuwai ya rasu bayan harin ‘yan bindiga a titin Wukari zuwa Zakibiam

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Benuwai (SSG), Farfesa David Salifu, ya rasu bayan samun rauni daga harbin bindiga a wani hari da 'yan bindiga suka ƙaddamar akan hanyar Wukari zuwa Zakibiam da ke tsakanin jihohin Benuwai da Taraba. Rahotanni sun bayyana cewa, farfesan, wanda shi ne SSG a zamanin mulkin tsohon gwamna Gabriel Suswam, ya rasu ne a safiyar ranar Juma'a a lokacin da ake masa magani a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Benuwai da ke Makurɗi bayan harin na ranar Alhamis. Al'amarin ya auku ne a lokacin da marigayin ke kan hanyar tafiya daga…
Read More

Bayern na shirin ninka albashin Michael Olise, zai kai daidai da na Kane

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayern Munich na ƙoƙarin ƙara wa wa'adin ɗan wasanta Michael Olise tsawo yayin da Real Madrid da PSG suke nuna kwaɗayi akansa. Akan haka ne Munich ta fara shirin masa tayin sabon kwantaragi da zai kai wa'adin nasa zuwa Yunin 2031, wanda zai ɗaga albashinsa na shekara-shekara daga Yuro miliyan 12 zuwa kusan Yuro miliyan 25, lamarin da zai sa ya yi kankankan da 'yan wasa Harry Kane da Jamal Musiala. Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da Olise ya yi gagarumin ƙoƙari wa Bayern a kakar wasa…
Read More

Amurka ta janye sojojinta a Nijeriya bayan wata shida

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Amurka ta janye da dama daga cikin dakarun tsaronta da ta tura wa Nijeriya domin aikin haɗaka da dakarun tsaro na daƙile ayyukan ta'addanci a yankin Tafkin Chadi, yayin da take cigaba da aiki tare da ƙasar akan lamuran leƙen asiri da wasu harkokin tsaro da hukumomin Nijeriya. Kwamandan sojojin saman Amurka a Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson ne ya sanar da haka a wata tattaunawa da manema labarai akan sakamakon babban taron jagororin tsaron ƙasashen Afirka na 2026. Ya ce, haɗakar ta tsakanin Washington da Abuja za ta cigaba da gudana musamman…
Read More

Iya Alakara: Tinubu ya yi wa Oluremi ba’a yayin cece-kucen sayar da ƙosai

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya nishaɗantar da jama'a a wajen wani taro da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, bayan da ya kira Uwargidansa, Sanata Oluremi Tinubu da "Iya Alakara", wato Mai ƙosai ko Mamar ƙosai. Tinubu ya furta haka ne a wani yanayi na barƙwanci yayin da yake gabatar da manyan baƙi a wajen liyafar da aka shirya wa 'yan jaridar fadar. Kalaman shugaban ƙasar na zuwa ne bayan cece-kucen da suka biyo bayan shawarar da Oluremi ta ba mata da su rungumi ƙananan sana'o'i kamar su sayar da ƙosai, masara gasassa,…
Read More

Gwamnatin Zamfara ta yaba wa Shugaban NAHCON kan nasarar ayyukan Hajjin 2026

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Jihar Zamfara ta jinjina wa Shugaban Hukumar Jigilar Alhazan Nijeriya (NAHCON), Ambasada Isma'il Abba Yusuf bisa ƙoƙarinsa wajen tabbatar da cimma nasarorin ayyukan Hajjin 2026 da ya gudana. A wata takarda da hukumar gudanarwar NAHCON ta fitar a ranar Juma'a, an bayyana cewa wata tawaga daga gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Daraktan Filin jiragen sama na Gusau, Alhaji Kabiru Yahaya Gusau ne ta bayyana haka yayin ziyartar ga Ambasada Isma'il Abba a ranar Alhamis. Daga cikin 'yan tawagar da Gwamna Dauda Lawal ya aike akwai Darakta kuɗi da rabawa, Alhaji Yahuza Mai Haja; Daraktan…
Read More

Kotu ta yi watsi da buƙatar bada belin neman maganin El-Rufa’i yayin da Asibitin Ƙasa ya musanta rahoton lafiya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Babbar Kotun Jihar Kaduna ta yi watsi da buƙatar beli da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya gabatar, bayan Asibitin Ƙasa da ke Abuja ya musanta rahoton lafiyar da aka gabatar domin tallafa wa buƙatar. Rahotanni sun bayyana cewa, an miƙa rahoton lafiyar ne a matsayin hujja don neman a bada belin El-Rufai, amma Asibitin Ƙasa ya bayyana cewa rahoton ba daga gare shi ya fito ba, lamarin da ya jefa sahihancinsa cikin shakku. Hukumar ICPC a wata sanrwa, ta ce tsohon gwamnan ya gabatar da rahoton lafiyar ne a matsayin hujjar buƙatar…
Read More

Gwamnatin Kebbi ta raba motocin taki da iri 110 kyauta ga manoma

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamnatin Jihar Kebbi ta raba motoci guda 110 na taki da kuma ton ɗari na irin zamani ga manoma 120,000 don noman damina na wannan shekara. Wannan yana daga cikin kudurran gwamna Malam Nasir Idris na haɓaka harkokin noma da kuma sauƙaƙa wa al'umma rage tsadar rayuwa musamman abinci a jihar. Gwamna Malam Nasir Idris ya bayyana cewa sanin kowa ne kashi tamanin na al'ummar jihar Kebbi sun dogara ne da noma saboda haka sun fi buƙatar tallafi a wannan ɓangaren, an kuma yi tsarin rabon takin da irin ta yadda zai isa ga ainihin…
Read More

Kano: Yadda likita ya rasu bayan minti biyar da isa duba marasa lafiya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani ƙwararren likita a Jihar Kano ya yanki jiki ya faɗi kuma ya rasu mintina 15 bayan zuwa wajen duba marasa lafiya da suka jima suna jiran sa a wani asibiti. Mai taimaka wa Gwamnan Jigawa, Sulaiman Harbo ne ya bayyana haka ga jaridar NewsPointNigeria bayan ganin yadda al'amarin ya auku a lokacin da ya kai dattijuwar mahaifiyarsa asibiti domin duba lafiyarta. Al'amarin ya faru ne a ranar Asabar a Asibitin Arewa Surgery Hospital da ke yankin Hotoro a Ƙaramar Hukumar Nasarawa, inda aka nemi marigayin likitan da ya maye gurbin wani abokin aikinsa…
Read More