Babaji

4782 Posts

Gwamnatin Trump za ta yi matuƙar sanya ido a zaɓukan Nijeriya na 2027, inji ɗan majalisar Amurka

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore ya ce gwamnatin ƙasar za ta bibiyi tare da sanya ido a babban zaɓen Nijeriya na 2027, yana mai cewa shi da Shugaba Donald Trump za su kasance masu kula da yadda za a gudanar da zaɓen. Moore, wanda ɗan jam'iyyar Republican da ke wakiltar Virginia ta Yamma ne, ya bayyana haka ne a wata hira ta gidan talabijin na Noire a rana Lahadi a lokacin da yake amsa tambayoyi akan zaɓen Nijeriya da ke tafe. A cewarsa, Washington za ta kula sosai da hanyoyin da za bi…
Read More

Mummunan hatsari ya yi ajalin ‘ya’yan tsohon mataimakin gwamnan Bauchi biyu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bacula, Sanata Baba Tela ya shiga halin jimami sakamakon rasuwar 'ya'yansa guda biyu, Mustapha da Ummi a wani mummunan hatsarin da ya auku a titin Bauchi zuwa Azare. Rahotanni sun bayyana cewa, mamatan sun rasu ne a yayin da suke koma wa Bauchi daga Azare. Sauran waɗanda suke cikin motar sun jikkata inda a halin yanzu suke karɓar magani. An ruwaito cewa, 'ya'yan tsohon mataimakin gwamnan sun rasu ne a nan take a sa'ilin da al'amarin ya faru, lamarin da aka tabbatar bayan kai gawarwakinsu wani asibiti a Bauchi. An…
Read More

Girgizar ƙasar Venezuela: Adadin waɗanda suka rasu ya kai 3,000

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Venezuela ta ce adadin mutanen da aka tabbatar mutuwarsu sakamakon munanan girgizar ƙasa guda biyu da suka auku a ƙarshen watan da ya gabata a kasar ya kai 3,000. Rahotanni sun bayyana cewa, har yanzu ana cigaba da bincike domin gano sama da mutum 40,000 da ba a san inda suke ba. Haka kuma, masu aikin ceton gaggawa a arewacin Venezuela na cigaba da aikin zaƙulo gawarwaki daga ƙarƙashin baraguzan gine-ginen da suka rushe a sanadiyyar faruwar al'amarin. Shugaban majalisar dokokin ƙasar, Jorge Rodriguez, wanda kuma ɗan uwa ne ga shugabar riƙon ƙwarya…
Read More

Boko Haram ta ƙone motoci da kayan miliyoyi Naira a sabon harin Yobe

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari a garin Geidam da ke Ƙaramar Hukumar Geidam t Jihar Yobe, inda suka ƙone motoci huɗu, ciki har da babbar mota da ke ɗauke da kayayyakin 'yan kasuwa na miliyoyin Naira. Rahotanni sun bayyana cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:30 na safiyar Juma'a yayin da al'umma ke shirin gudanar da sallar asubahi. Maharan sun fara kai hari sakatariyar ƙaramar hukumar inda suka ƙone motar Toyota Hilux da wata motar bus mallakin ƙaramar hukumar, kafin daga bisani su ƙone wata babbar mota da ke ɗauke da kayan…
Read More

Babu diyya ga kadarorin da ‘yan Nijeriya suka bari, inji gwamnatin Afirka ta Kudu

Gwamnatin Afirka ta Kudu ta bayyana cewa, ba za ta biya ’yan Nijeriya diyya ba akan kadarorin da suka bari a ƙasar bayan an kwashe su zuwa Nijeriya. Gwamnatin ta jaddada cewa duk wata kadara da aka mallaka ba bisa ka’ida ba, ko kuma wadda ke cikin matsugunan da ba su da izinin gwamnati (informal settlements), ba za ta cancanci a biya mata kowace irin diyya ba. Wannan matsaya ta sake fitowa ne daga bakin Ministar da ke Fadar Shugaban Ƙasa ta Afirka ta Kudu, Khumbudzo Ntshavheni, wadda ta yi watsi da ra'ayin cewa gwamnatin Pretoria za ta biya ’yan…
Read More

Kofin Duniya: Moroko ta kai wasan dab da na kusa da na ƙarshe bayan lallasa Kanada

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Moroko ta sake nuna bajintarta a gasar Kofin Duniya da ke gudana a Nahiyar Amurka bayan da ta lallasa ɗaya daga cikin masu masaukin baƙi, Kanada da ci 3 da 0 wasan zagayen 'yan 16. Ɗan wasan Atlas Lions, Azzedine Ounahi ya samu zura ƙwallo biyu a ragar Kanada, yayin sa Soufiane Rahimi da ya zo daga benci ya zura ta ukun ana gab da kammala wasan. Haka ma Kyaftin, Achraf Hakimi da Brahim Diaz na Real Madrid, waɗanda sun taka rawar gani wajen kai farmaki inda suka bayar da ƙwallo biyun da…
Read More

Argentina ta yi waje da Cape Verde bayan wasa mai zafi a zagayen ‘yan 32

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Argentina ta samu tikitin zuwa zagayen 'yan 16 a gasar Kofin Duniya bayan doke Cape Verde da ci 3 da 2 a wani wasa mai cike da armashi. Duk da cewa Cape Verde ta yi rashin nasara, ƙungiyar ta nuna ƙwazo da jajircewa, inda ta tilasta wa fitacciyar ƙasar ta Kudancin Amurka yin aiki tuƙuru kafin ta tabbatar da nasarar. Wasan ya kasance mai cike da hare-hare, inda Cape Verde ta cigaba da matsa lamba har zuwa mintunan ƙarshe, lamarin da ya sa Argentina ta sha wahala wajen kare jagorancinta. Nasarar ta tabbatar…
Read More

Fadar Shugaban Ƙasa ta umarci hukumomin tsaro su binciki waɗanda ke da hannu a badaƙalar hukumar bogi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Fadar Shugaban Ƙasa ta yi kira ga hukumomin EFCC DSS da NPF da su gudanar da binciken gano waɗanda ake zargi haɗa hannu da su wajen ba wa Adeyemi Adeniyi Matthew damar aiki da hukumar bogi ta "Presidential Foreign Intervention Promotion Council" (PCFIPC). Rahotanni sun bayyana cewa, fadar a wata sanarwa da Mai Taimaka wa Shugaban Ƙasa akan Harkokin Yaɗa Labarai, Temitope Ajayi ya wallafa a kafar X ranar Asabar, ta ce wajibi ne a gano waɗanda suke da hannu a taimaka wa Adeniyi aiki da hukumar ƙasa ta bogi, a dakatar da kuma…
Read More

Sakkwato: ‘Yan bindiga sun halaka hakimi, ɗansa da wasu biyar yayin da matasa suka tare babban titi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu 'yan bindiga sun halaka Hakimin yankin Kulodo da ke Ƙaramar Hukumar Bodinga a Jihar Sakkwato, Alhaji Abubakar Tudu, tare da babban ɗansa da wasu mutum huɗu a wani sabon hari da suka ƙaddamar a ƙauyukan Kulodo da Kwance. Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun kutsa cikin ƙauyukan ne tare da kai farmaki kan mazauna yankin, lamarin da ya yi sanadin asarar rayuka da tayar da fargaba acikin jama'ar yankin. Haka kuma, hari ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda wanda mazaunin ƙauyen Kwance ne, lamarin da ya matasa da dama suak yi cincirindo suak…
Read More

‘Suna sauya ma’anar kalamaina’: Akpabio ya faɗi dalilinsa na daina kallon talabijin

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya ce ya daina kallon talabijin ne saboda ana sauya ma'anonin kalamansa, yana mai cewa an jirkita ma'anonin kalamansa na kwanan nan akan ababen more rayuwa na gwamnatin Shugaba Bola Tinubu. Akpabio ya bayyana haka ne a ranar Juma'a yayin ƙaddamar da wasu titina a yankin Karsana da ke Abuja, inda ya bayyana cewa kalaman nasa sun taƙaitu ne kaɗai akan ayyukan da aka aiwatar a Abuja ba baki ɗaya ƙasar ba. Ya ce, kalaman nasa na farko suna magana ne akan adadin ayyukan da aka ƙaddamar a birnin…
Read More