Babaji

4780 Posts

Kaduna: Hare-haren ‘yan bindiga sun yi ajalin manoma 9 da garkuwa da mutane da dama

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Asabar ne 'yan bindiga sun halaka kimanin manoma guda tara da kuma yin awon-gaba da wasu da dama a wasu hare-haren gonaki da ke a bayan garin ƙauyen Kakangi a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari da ke Jihar Kaduna. Rahotanni sun bayyana maharan sun buɗe wa manoman da ke aiki a gonakinsu wuta a lokacin da suka riske su suna bakin aiki, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum tara, kafin daga bisani suka tafi da wasu da ba a tantance adadinsu ba. Al'amarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3 na yamma…
Read More

Sabbin bayanai sun alaƙanta ofishin sakataren gwamnati da daraktan hukumar bogi yayin da Majalisar Dattawa za ta yi zama akan kasafin biliyan N1.3

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An samu sababbin bayanai sun bjiro da ke nuna Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (OSGF) ya amince da Daraktan Hukumar Shugaban Ƙasa ta Ciyar da Lamuran Harkokin Waje Gaba (PFIPC) ta bogi, Mista Adeniyi Adeyemi, ya halarci Taron Canada-Africa Fintech (CAFS) a watan Agustan 2025. Wannan al'amari na zuwa ne a daidai lokacin da ake cece-kuce ciki har da allah-wadai daga tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da kuma neman a bayyana haƙiƙanin gaskiyar al'amarin daga ɓangaren Cibiyar Tabbatar da Gaskiya da Adalci akan Albarkatun Ƙasa (SERAP) akan ware Naira biliyan 1.3 ga hukumar bogin…
Read More

Idan Tinubu ya lashe zaɓen 2027 sai na halaka ɗansa Seyi, inji DJ Chicken

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanannen mai nishaɗantarwa a Soshiyal Mediya da ake kira da DJ Chicken ya janyo cece-kuce a kafafen sada zumunta sakamakon furta wasu kalamai masu hatsari akan sake zaɓar Shugaba Bola Tinubu a karo na biyu. DJ'n ya yi haka ne a wani bidiyo ta shafinsa na Instagram duk da cewa daga bisani an goge shi, inda ya yi iƙirarin cewa Shugaba Tinubu ba zai lashe zaɓen da ke tafe ba. Sannan, ya kuma yi barazana mai tayar da hankali akan ɗan Shugaban Ƙasar, Seyi Tinubu, inda aka ga yadda ɗan mediyar ya yi shiga…
Read More

Kofin Duniya: Bellingham ya zura biyu yayin da ‘yan Ingila 10 suka doke Mexico

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Ingila ta sha da ƙyar a hannun Mexico a zagayen 'yan 16 na gasar Kofin Duniya na 2026 yayin da aka kammala wasan tsakaninsu da 3 da 2, lamarin da ya ba ta damar zuwa zagayen wasan dab da na kusa da na ƙarshe. Ɗan wasan Real Madrid, Jude Bellingham ne ya zura ƙwallo biyu, wanda hakan ya ba ƙasar damar jan ragamar wasan, kana daga bisani Julian Quinones na Mexico ya goge ɗaya. Bayan an sallami Jarell Quansah daga wasan ne sai Ingila ta samu damar ƙara ta uku a bugun daga…
Read More

Kofin Duniya: Norway ta kai wasan dab da na kusa da na ƙarshe a karon farko bayan doke Brazil

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Norway ta shiga sahun ƙasashen da suka kafa tarihi a harkar wasan ƙwallon ƙafa na zamani bayan doke Brazil da ci 2 da 1 a wasan zagayen 'yan 16 na gasar Kofin Duniya na 2026. Wannan shi ne karo na farko da Norway ta kai zagayen wasan dab da na kusa da na ƙarshe a gasar, kamar yadda ita ma Brazil wannan shi ne karon farko da aka cire ta zagayen tun a 1990. Da fari, ɗan wasa Bruno Gumarães ne ya zubar da bugun fenarati bayan dogon lokaci da sashen binciken VAR…
Read More

‘Ku nuna mana hujjar’: Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da iƙirarin kashe tiriliyan N8 da ba su cikin wajen kasafin kuɗi

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin cewa ta kashe sama da Naira tiriliyan 8 a wajen kasafin kuɗin shekarar 2026, tana mai cewa babu wata hujja da ke tabbatar da hakan. Ministan kuɗi, Taiwo Oyedele, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce an yi wa kalaman wakilin Asusun Lamuni na Duniya (IMF) a Najeriya, Christian Ebeke, mummunar fassara. Oyedele ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ba ta da abin da ake kira “kasafin kuɗi na ɓoye”, yana mai jaddada cewa duk kuɗaɗen gwamnati ana kashe su ne bisa dokokin kasafin kuɗi da majalisar tarayya ta amince da su.…
Read More

Waɗanda ambaliyar Mokwa ta rutsa da su sun yi wa EFCC da ICPC ƙorafi kan zargin sauya akalar kuɗaɗen tallafi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu daga cikin mutanen da ambaliyar ruwa a Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja ta shafa, sun yi ƙorafi ga hukumomin EFCC, ICPC da kuma Rundunar ’Yan Sanda, inda suka buƙaci a gudanar da cikakken bincike akan yadda aka karba da kashe kuɗaɗe da kayan tallafin da aka tara domin taimaka musu. Wannan mataki ya biyo bayan zarge-zargen da ake yi ne na karkatar da biliyoyin nairori da kayan agajin da aka ware domin tallafa wa waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a shekarar 2025. Daga cikin ƙorafin da aka gabatar a ranar 26 ga…
Read More

Mashigar Hormuz: Iran ta ba tankokin jigilar mai sabon umarni

Iran ta yi gargaɗi ga dukkan jiragen ruwa da tankokin ɗaukar mai da ke bi ta Mashigin Strait of Hormuz cewa su yi amfani ne kawai da hanyoyin da hukumominta suka amince da su, tana mai cewa duk wanda ya saɓa zai fuskanci "martani mai ƙarfi cikin gaggawa." Sanarwar ta fito ne daga rundunar haɗin gwiwar sojojin Iran, wadda ta ce duk wani jirgin ruwa da ya kauce wa hanyoyin da aka tsara ko ya yi watsi da umarnin kewayawa zai iya jefa tsaron jirginsa cikin haɗari. Gargaɗin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawar…
Read More

Gwamnatin Trump za ta yi matuƙar sanya ido a zaɓukan Nijeriya na 2027, inji ɗan majalisar Amurka

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore ya ce gwamnatin ƙasar za ta bibiyi tare da sanya ido a babban zaɓen Nijeriya na 2027, yana mai cewa shi da Shugaba Donald Trump za su kasance masu kula da yadda za a gudanar da zaɓen. Moore, wanda ɗan jam'iyyar Republican da ke wakiltar Virginia ta Yamma ne, ya bayyana haka ne a wata hira ta gidan talabijin na Noire a rana Lahadi a lokacin da yake amsa tambayoyi akan zaɓen Nijeriya da ke tafe. A cewarsa, Washington za ta kula sosai da hanyoyin da za bi…
Read More

Mummunan hatsari ya yi ajalin ‘ya’yan tsohon mataimakin gwamnan Bauchi biyu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bacula, Sanata Baba Tela ya shiga halin jimami sakamakon rasuwar 'ya'yansa guda biyu, Mustapha da Ummi a wani mummunan hatsarin da ya auku a titin Bauchi zuwa Azare. Rahotanni sun bayyana cewa, mamatan sun rasu ne a yayin da suke koma wa Bauchi daga Azare. Sauran waɗanda suke cikin motar sun jikkata inda a halin yanzu suke karɓar magani. An ruwaito cewa, 'ya'yan tsohon mataimakin gwamnan sun rasu ne a nan take a sa'ilin da al'amarin ya faru, lamarin da aka tabbatar bayan kai gawarwakinsu wani asibiti a Bauchi. An…
Read More