ukarofi

11605 Posts
Ba mu da ƙarancin ma’aikata da kayan aiki a asibitin ƙwararru na Gombe – Daraktan asibitin 

Ba mu da ƙarancin ma’aikata da kayan aiki a asibitin ƙwararru na Gombe – Daraktan asibitin 

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Asibiitn ƙwararru na jihar Gombe shi ne mafi daɗewar asibiti a fadar jihar da aka gina shi tun kafin samun ‘yancin kan Nijeriya a shekarar 1958, kuma asibitin ya samu canje-canje sosai domin an fara shi ne tun daga matakin dispensary, ya koma cibiyar lafiyar matakin farko Primary Health Center, daga baya ya zama General sannan aka mayar da shi asibitin ƙwararru wato Specialist. Jin ana kukan cewa asibitin yana fama da ƙarancin kayan aiki da ƙwararrun ma’aikata, wakilinmu ya ziyarci asibiti inda ya zanta da Daraktan Asibitin Dokta Mu’azu Shu’aibu Ishaƙa, don jin…
Read More
Sarkin Gona ya yi kira ga gwamnati da masu kuɗi wajen taimakon masu ƙaramin ƙarfi

Sarkin Gona ya yi kira ga gwamnati da masu kuɗi wajen taimakon masu ƙaramin ƙarfi

Daga Abubakar A Bolari, a Gombe Mai martaba Sarkin Gona da ke yankin Ƙaramar Hukumar Akko a jihar Gombe, Alhaji Umar Abdulkadir Abdussalam, ya yi kira ga gwamanti da masu hannu da shuni da cewa a dinga taimakon masu ƙaranin ƙarfi ganin cewa rayuwa ta yi tsanani. Sarkin Gona, ya ce taimako ya yi ƙarancin al'umma na cikin matsin rayuwa hakan tasa  matasa masu tasowa ke zama barazana a cikin al'umma. Mai martaba ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar sa inda yace dole sai gwamanti ta tashi tsaye tayi abunda ya dace…
Read More
Shettima ya buƙaci likitocin Nijeriya su taimaka wajen inganta ƙasar

Shettima ya buƙaci likitocin Nijeriya su taimaka wajen inganta ƙasar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mataimakin Shugaban Ƙasar Nijeriya, Kashim Shettima ya yi kira ga likitocin ƙasar, su riƙa zama a ƙasar, don taimaka wa magance matsalar da ƙasar ke fuskanta ta ƙarancin likitoci. Shettima ya yi kiran ne a lokacin da ƙungiyar likitocin ƙasar - ƙarƙashin jagorancin sabon shugabanta, Farfesa Bala Audu - suka kai masa ziyara a ofishinsa ranar Talata. Mataimakin shugaban ƙasar ya nuna damuwa kan yadda likitocin ƙasar ke yawan ficewa daga ƙasar domin neman ayyuka a ƙasashen waje. A baya-bayan nan dai ana samun yawaitar ficewar likitocin Nijeriya daga ƙasar, zuwa ƙasashen wajen domin…
Read More
Ta ƙona mahaifiyarta ‘yar shekara 86 kan zargin jefa ta a ƙangin talauci

Ta ƙona mahaifiyarta ‘yar shekara 86 kan zargin jefa ta a ƙangin talauci

Wata mata 'yar shekara 45 mai suna Abiodun ta banka wa mahaifiyarta ’yar shekara 86 wuta a garin Ondo da ke Ƙaramar Hukumar Ondo ta Yamma a Jihar Ondo. Abiodun, wadda aka fi sani da ‘Iya Sunday’ ta ce ta ƙona mahaifiyarta ne saboda zargin ta da zamowa silar wahalhalunta a rayuwa. Wani ganau mai suna Sola Oladele ya bayyana cewa wadda ake zargin ta zo gidan mahaifiyarta ne a ranar Juma’a da misalin ƙarfe 5 na safe ta kira ta kafin ta zuba mata man fetur sannan ya banka mata wuta. Ganau ɗin ya ce, matar da faɗa masa…
Read More
Kotu ta tasa ƙeyar jami’an EFCC na bogi zuwa gidan yari

Kotu ta tasa ƙeyar jami’an EFCC na bogi zuwa gidan yari

Kotu ta yanke hukuncin ɗaurin shekaru 30 ga wasu mutane biyu da aka kama suna yin sojan gona a matsayin jami’an hukumar  (EFCC. Dubun jami’an EFCC na bogi, Ugwu Chijioke da Ibrahim Adekunle, ta cika ne a lokacin da suka je domin zartar da wani jabun umarnin kotu a unguwar Lekki da ke Legas a watan Mayun 2021. Abubuwan da aka kama a hnnun waɗannan jami’an EFCC na bogi sun hada da jabun katin shaidar aiki da rigunan hukumar da kuma takardar umarnin gobi daga Kotun Majistare da ke zamanta a Mushin. Hukumar ta gurfanar da su a gaban Kotun…
Read More
Ɗan sanda ya harbe alƙali ana tsaka da shari’a a kotu

Ɗan sanda ya harbe alƙali ana tsaka da shari’a a kotu

Wani babban jami'in 'yan sandan Kenya ya harbi mai jagorantar shari'a a wata kotun majistare da ke Nairobi, babban birnin ƙasar Kenya. Ɗan sandan mai muƙamin babban Isfekta ya buɗe wa mai shari'a Monica Kiɓuti wuta jim kaɗan bayan ta yanke wa matarsa hukunci kan wani laifi da ake zarginta da aikatawa. Rahotonni sun ce jami'in ɗan sandan ya fusata ne bayan da kotun ta ƙi amincewa da buƙatar belin matar tasa. Daga nan ne, Sufeto Samson Kipchirchir Kipruto, wanda ke jagorantar ofishin 'yan sanda na Londiani da ke yammacin ƙasar, ya zaro bindigarsa tare da harbe alƙalin inda ya…
Read More
Amurka ta ce a fusace ta ke da Chana kan goyon bayan Rasha a yaƙin Ukraine

Amurka ta ce a fusace ta ke da Chana kan goyon bayan Rasha a yaƙin Ukraine

Amurka ta cacaki Ƙasar Chana da game da zargin bai wa Rasha tallafi da kuma goyon bayanta a yaƙin da ta ke yi da Ukraine. Da ya ke bayyana takaicinsa game da batun, sakataren harkokin wajen ƙasar Antony Blinken, ya ce lokaci ya yi da ya kamata duniya ta juyawa Chana baya, har sai ta tsame hannunta daga tallafa wa Rahsa a wannan yaƙi. A mabambantan lokuta dai, Chana ta sha musanta zargin bai wa Rasha tallafi ta kowaccce fuska game da yaƙin, to sai dai Blinken wanda ke magana gaban wani taron manema labarai tsakanin sa da shugaban ƙungiyar…
Read More
Faransa na karɓar baƙuncin taron tallafa wa Afrika don samar da rigakafin cutuka

Faransa na karɓar baƙuncin taron tallafa wa Afrika don samar da rigakafin cutuka

A Alhamis ɗin nan ce, ake fara taron ƙasa da ƙasa a birnin Paris don tallafa wa Afrika wajen samar da alluran rigakafin cutuka, domin taimaka wa ƙasashen nahiyar cimma muradun samun kariya daga kamuwa da cutuka da kuma inganta lafiya nan da zuwa shekarar 2030. An shirya gudanar da taron ne a ƙarƙarshin haɗin gwiwar gwamnatin Faransa da ƙungiyar ƙasashen Afirka AU, sai ƙwararru daga ƙasashen Turai, da kuma shirin Gaɓi da ke taimaka wa wadatar alluran rigakafi ga yara a ƙasashe marasa ƙarfi. Muhimmin batun da taron zai mayar da hankali akai shi ne kafa gidauniyar maƙudan kuɗaɗen…
Read More
Canada ta ayyana rundunar IRGC ta Iran cikin jerin ƙungiyoyin ‘yan ta’adda

Canada ta ayyana rundunar IRGC ta Iran cikin jerin ƙungiyoyin ‘yan ta’adda

Ƙasar Canada, ta sanya sunan rundunar Juyin-juya hali ta Ƙasar Iran IRGC, cikin jerin ƙungiyoyin ‘yan ta'adda, inda ta buƙaci ‘yan ƙasarta da ke Iran ɗin su fice. Gwamnatin Kanada ta sanar da hakan ne a ranar Laraba, tana mai bayyana matakin a matsayin wani ɓangare na yakin da Ottawa ke yi da ta'addanci. ‘Yan siyasar ƙasar ta Canada sun jima suna fatana ganin an aiwatar da wannan mataki, wanda ke nufin za a hana dubban manyan jami'an rundunar ta IRGC shiga ƙasar. Shekaru da dama, 'yan adawa masu ra'ayin mazan jiya a Canada sun buƙaci Firaminista Justin Trudeau, da…
Read More
Mun bankaɗo makircin APC na son ƙwace Jihar Ribas – PDP

Mun bankaɗo makircin APC na son ƙwace Jihar Ribas – PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta ce, makirce-makircen da Jam’iyyar APC mai mulkin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ke yi na ƙwace Jihar Ribas da ƙarfin tsiya ya kai intaha na ƙoƙarin ƙwace jihar da ƙarfin tsiya daga PDP, amma ta ce hakan ba zai cimma nasara ba. A ranar Laraba ne shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Ribas suka buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci a jihar, bisa zargin cewa jihar na cikin yanayin tashin-tashina. Shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar APC, Tony Okocha ne ya yi wannan kiran a yayin wani taron manema…
Read More