15
May
Daga LUBABATU LEI Ta hanyar amfani da tashoshin sadarwa na wayoyin salula da manhajojin waya da yanar gizo da dai sauransu, bisa fasahohinta na zamani, Amurka ta daɗe da yi wa gwamnatocin ƙasa da ƙasa da kamfanoninsu da ma al’ummarsu leken asiri, ciki har da ƙasashen Afirka, muna iya cewa, ta amsa sunanta na babbar ɓarauniyar satar bayanai. Sai dai a kwanan nan, barauniyar ce take sake yin kiran a kama barawo, inda mataimakiyar sakataren harkokin wajen ƙasar ta Amurka Wendy Sherman a ziyararta a nahiyar Afirka, ta ce wai, yadda wasu ƙasashen Afirka suka zabi kamfanin Huawei na ƙasar…
