Kasashen Waje

Jakadan Sin ya yi kira a bada fifiko wajen bunƙasa cigaban yankin Sahel

Jakadan Sin ya yi kira a bada fifiko wajen bunƙasa cigaban yankin Sahel

Daga CMG HAUSA Wakilin ƙasar Sin ya buƙaci a bada fifiko wajen bunƙasa cigaban yankin Sahel. Zhang Jun, zaunannen wakilin ƙasar Sin a MƊD, ya ce Afrika tana fuskantar wahalhalu wajen cimma nasarar samun cigaba. Matsalolin ƙarancin abinci da duniya ke fuskanta a halin yanzu, da matsalar makamashi, da ta kuɗaɗe, sun kara tsananta halin da ake ciki a Afrika, sannan matsalar ta fi kamari a yankin Sahel. Zhang Jun, ya bayyana hakan ne a yayin taron kwamitin sulhun MƊD game da shirin G5 Sahel, wato wani shiri ne na hadin gwiwa don tsara manufofin bunƙasa cigaba da tabbatar da…
Read More
Shugaba Xi ya jaddada aniyar ƙasarsa ta buɗe ƙofa mai nagarta

Shugaba Xi ya jaddada aniyar ƙasarsa ta buɗe ƙofa mai nagarta

Daga CMG HAUSA A yau Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada aniyar ƙasar sa ta buɗe kofa mai nagarta, yana mai cewa Sin za ta ci gaba da bude kofa ga duniya baki ɗaya, ba tare da sauya matsaya ba. Xi ya yi wannan tsokaci ne, yayin da yake jawabi ga taron cika shekaru 70, da kafuwar hukumar yayata hada-hadar cinikayyar ƙasa da ƙasa, da taron kolin ƙasa da ƙasa na ingiza harkokin cinikayya da zuba jari, da ya gudana ta kafar bidiyo. Fassarwa: Saminu
Read More
NED—Makamin mallakar duniya

NED—Makamin mallakar duniya

Daga AMINA XU Asusun demokuraɗiyya na Amurka wato NED, ‘yan siyasar ƙasar sun yi masa laƙabin “ƙungiya mai zaman kanta dake baiwa sauran ƙasashe taimakon demokuraɗiyya”. Amma a haƙiƙa dai fadar White Housa da ma majalisar dokokin ƙasar na samar masa kuɗi, kuma asusun yana bin umurnin gwamnatin ƙasar wajen jagorantar ƙungiyoyin masu zaman kansu na ƙasa da ƙasa da su yayata manufofin Amurka da hambarar da mulkin ƙasashen ta hanyar samar musu kuɗaɗe. Hakan ya sa ya kasance wani makami mai ƙarfi na Amurka don cin moriyarta da mallakar duniya. Mai zana: Amina Xu
Read More
BBC ta kitsa ƙarairayi kan batun ta’addanci

BBC ta kitsa ƙarairayi kan batun ta’addanci

Daga CMG HAUSA Kwanaki sama da 20 da suka gabata, an kai farmakin ta’addanci kan wata mota ta kwalejin koyon harshen Sinanci, wato Confucius Institute dake jami’ar Karachi dake ƙasar Pakistan, al’amarin da ya haddasa mutuwar wasu malaman ƙasar Sin uku, tare da jikkata wani. Kwamitin tsaron Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi Allah wadai da irin wannan farmakin da kakkausar murya. Amma ita kafar yaɗa labaran BBC, ta wallafa wasu rahotanni kwanan nan, inda ta yi yunkurin wanke waɗanda suka kai farmakin daga mummunan laifin da suka aikata. A matsayinta na ɗaya daga cikin kafafen yaɗa labaran ƙasashen yammacin duniya…
Read More
Sanarwar ministocin ƙungiyar G7 ta keta ƙa’idar ƙasa da ƙasa ce dake neman rura wutar rikici

Sanarwar ministocin ƙungiyar G7 ta keta ƙa’idar ƙasa da ƙasa ce dake neman rura wutar rikici

Daga FAEZA MUSTAPHA A baya-bayan nan ne, ministocin harkokin wajen ƙasashen ƙungiyar G7 suka fitar da wata sanarwa bayan taron da suka yi, inda a cikinta suka bayyana wasu buƙatu ga ƙasar Sin, waɗanda suka yi su bisa son zuciya da zarge-zarge marasa tushe, da gazawa wajen mutunta cikakken ’yancin kan ƙasar. Cikin sanarwar, sun ce sun damu da yanayin kwanciyar hankali a tsibirin Taiwan. Amma sam ƙasashen yamma ba su damu da hakan kamar yadda suke furtawa ba. Sanin kansu ne cewa, zaman lafiyar yankin ya dogara ne da janyewarsu daga yi wa harkokin gidan Sin katsalandan da kuma…
Read More
An cimma nasarar kawar da ƙwayoyin cutar COVID-19 baki ɗaya a ƙananan hukumomi 16 na birnin Shanghai

An cimma nasarar kawar da ƙwayoyin cutar COVID-19 baki ɗaya a ƙananan hukumomi 16 na birnin Shanghai

Daga CMG HAUSA A yayin taron ganawa da manema labarai game da aikin kandagarkin annobar COVID-19 da aka shirya yau Talata da safe, an bayyana cewa, a halin yanzu, an cimma nasarar kawar da ƙwayoyin cutar COVID-19 baki ɗaya a yankunan ƙananan hukumomi 16 dake birnin Shanghai na ƙasar Sin. A jiya Litinin 16 ga wata, an tabbatar da sabbin mutane 77 da suka kamu da cutar, sannan wasu mutane 746 da suka kamu da cutar, amma ba tare da nuna alamun cutar ba a birnin Shanghai. Kuma, dukkansu suna zaune ne a cikin yankunan da aka kilace. Bugu da…
Read More
Wa zai yarda Amurka ta goyi bayan yankin Taiwan don halartar babban taron lafiya na duniya?

Wa zai yarda Amurka ta goyi bayan yankin Taiwan don halartar babban taron lafiya na duniya?

Daga CMG HAUSA A gabannin babban taron ƙasa da ƙasa kan harkokin kiwon lafiya karo na 75, wasu ‘yan siyasar Amurka sun sake ƙulla makirci, na nunawa yankin Taiwan goyon baya don halartar taron. Kwanan nan ne, shugaban Amurka ya sa hannu kan wani shirin doka, inda ya buƙaci sakataren harkokin wajen ƙasar, da ya taimaki yankin Taiwan, don sake dawo da matsayinsa na dan kallo a hukumar WHO, ta yadda zai samu damar halartar taron. Irin wannan abu, shisshigi ne da aka yi cikin harkokin cikin gidan ƙasar Sin, wanda kuma ya sabawa babbar manufar kasancewar ƙasar Sin ɗaya…
Read More
Bayan wani mahaukacin ɗan bindiga sai mahaukaciyar ƙasa

Bayan wani mahaukacin ɗan bindiga sai mahaukaciyar ƙasa

Daga CMG HAUSA A yayin da mutane suka je kasuwa don sayen kayayyaki a ƙarshen mako, ba su san hawa ba balle sauke, sai kawai aka harbe su da bindiga. Wannan harin da ya abku ba gaira ba dalili shi ne abin da ake kira “hauka”. Wani saurayi farar fata mai shekaru 18 a duniya ne, ya ƙaddamar da wannan hari a ranar Asabar da ta wuce, a wata kasuwar zamani dake garin Buffalo na jihar New York ta ƙasar Amurka. Inda ya rika watsa hotunan bidiyon yadda yake kashe mutane kai tsaye a shafin yanar gizo. Cikin ‘yan mintuna…
Read More
Idan amarya ba ta hau doki ba, bai kamata a ɗora mata kaya ba

Idan amarya ba ta hau doki ba, bai kamata a ɗora mata kaya ba

Daga AHMAD FAGAM Ko shakka babu, duniyar bil adama tana fama da tarin ƙalubaloli waɗanda ke zama barazana ga zaman lafiya, da tsaro, da walwala, har ma da ci gaban duniyarmu baki ɗaya. Musamman idan muka yi la’akari da yadda duniyarmu ke fuskantar tarin matsaloli, kamar matsalar karayar tattalin arzkin sassa daban-daban na duniya, da matsalar sauyin yanayi wanda ke kara jefa rayuwar dan adam da sauran halittu gami da shi kansa muhallin halittun cikin garari, ga kuma matsalar annobar COVID-19 da ake fama da ita, sannan uwa uba ga matsalar yawaitar tashe-tashen hankula a sassa daban-daban na duniya. Sai…
Read More
Annobar COVID-19 ba za ta hana cigaban tattalin arzikin ƙasar Sin yadda ya kamata ba

Annobar COVID-19 ba za ta hana cigaban tattalin arzikin ƙasar Sin yadda ya kamata ba

Daga CMG HAUSA Tarukan manema labarai biyu da gwamnatin ƙasar Sin ta shirya da safiyar yau Litinin sun jawo hankali matuƙa daga bangarori daban-daban. Taro na farko, wanda hukumar ƙididdiga ta ƙasar Sin ta shirya, ya fitar da wasu muhimman alkaluman tattalin arzikin ƙasar a watan Afrilun bana. Duba da yadda halin da ake ciki a duniya ke canjawa, gami da yanayin annobar COVID-19 a cikin gida, tattalin arzikin ƙasar Sin na kara fuskantar matsin lamba, inda kakakin hukumar ya yi nuni da cewa, dalilin kuwa shi ne tasirin da annobar ta haifar na gajeren lokaci, amma ba zai hana…
Read More