Kasashen Waje

Sin ta himmatu wajen tabbatar da kafuwar yankin ciniki maras shinge na Asiya da Pacific

Sin ta himmatu wajen tabbatar da kafuwar yankin ciniki maras shinge na Asiya da Pacific

Daga CMG HAUSA Ministan maaikatar cinikiyya ta ƙasar Sin Wang Wentao, ya ce ƙasar sa za ta yi aiki tukuru, wajen tabbatar da nasarar kafa yankin ciniki maras shinge na Asiya da Pacific, cikakke kuma bisa matsayin koli. Minista Wang ya bayyana hakan ne cikin jawabinsa ta kafar bidiyo, yayin taro na 28 na ministocin ƙungiyar hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Pacific ko APEC, wanda ya gudana a ƙarshen mako. Wang ya ce kamata ya yi dukkanin ƙasashe mambobin APEC su jajirce, wajen gina alumma mai makomar bai daya a matsayin tushensu, su kuma ingiza haɗin gwiwa…
Read More
Masanin Nijeriya: Yadda Amurka da ƙasashen Yamma ke furta kalaman tsokana zai ƙara rashin zaman lafiyar duniya

Masanin Nijeriya: Yadda Amurka da ƙasashen Yamma ke furta kalaman tsokana zai ƙara rashin zaman lafiyar duniya

Daga CMG HAUSA Wani masanin ƙasar Najeriya, Joseph Peter Ochogwu, ya bayyana a yayin hira da ‘yan jarida cewa, Amurka da ƙungiyar NATO, suna cigaba da neman tada jijiyar wuya, da yin fito-na-fito, da bayyana kalaman tsokana, game da rikincin Rasha da Ukraine. Lamarin da ke kara ta’azzara ƙaruwar rashin zaman lafiya. Joseph Peter Ochogwu, farfesa ne a jami’ar Nile dake Najeriya, ya ce, NATO da ƙawayenta, suna kara haifar da tashin rikici, sannan tsadar farashin muhimmin kayan masarufi a duniya yana ƙara ƙamari, wanda hakan kadai yana iya yin sanadiyyar rashin zaman lafiya a sauye-sauyen fagen siyasar duniya. Ochogwu ya bayyana farin cikinsa…
Read More
Sin ta yi kira da a daidaita batun ‘yan guudun hijira yadda ya kamata

Sin ta yi kira da a daidaita batun ‘yan guudun hijira yadda ya kamata

Daga CMG HAUSA Mataimakin wakilin dindindin na ƙasar Sin dake Majalisar Dinkin Duniya, Dai Bing, ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, ya dace a daidaita batun ‘yan gudun hijira daga dukkan fannoni kuma yadda ya kamata, kana, ya zama dole a kawar da nuna bambanci da fin ƙarfi kan ‘yan gudun hijira, da daidaita sabani ta hanyar siyasa. Dai Bing ya bayyana a wajen muhawarar dandalin tattauna batun ‘yan gudun hijira na ƙasa da ƙasa karo na farko, cewa, babban dalilin da ya jawo matsalar ‘yan gudun hijira shi ne, rashin daidaiton ci gaba. Don haka ya ce, ya dace…
Read More
Wang Wenbin ya amsa tambayoyin manema labarai game da goyon-bayan da aka nunawa matsayin ƙasar Sin kan batun Taiwan a wajen taron WHO

Wang Wenbin ya amsa tambayoyin manema labarai game da goyon-bayan da aka nunawa matsayin ƙasar Sin kan batun Taiwan a wajen taron WHO

Daga CMG HAUSA Za a gudanar da babban taro karo na 75 na hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO daga ranar 22 zuwa 28 ga watan Mayun bana. Hukumomin kula da harkokin wajen yankin Taiwan sun nuna rashin jin daɗin game da rashin samun gayyatar halartar taron. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Sin, Wang Wenbin ya ce, Sin ƙasa ce ɗaya tak a duniya, kuma gwamnatin Jamhuriyar Jama’ar ƙasar Sin halastacciyar gwamnati ce ɗaya kaɗai dake wakiltar ƙasar. Taiwan kuma, wani ɓangare ne da ba za’a iya ware shi daga babban yankin ƙasar Sin ba. Ya ce…
Read More
Sin za ta gaggauta raya tsarin lambunan shan iska da na tsirrai

Sin za ta gaggauta raya tsarin lambunan shan iska da na tsirrai

Daga CMG HAUSA Rahotanni daga bikin tallata ranar kasancewar halittu daban-daban na duniya na shekara ta 2022 wanda aka yi a jiya Jumma’a a ƙasar Sin sun ce, ƙasar za ta gaggauta raya tsarin lambunan shan iska da lambunan tsirrai, kuma a shekarar da muke ciki, za ta ƙara gina wasu lambunan shan iska, da kammala tsara shirin raya lambunan tsirrai na ƙasa. Babban taken ranar kasancewar halittu daban-daban na duniya a bana shi ne, raya halittu masu kyakkyawar makoma ta bai daya a duniya. Sakamakon ƙoƙarin da aka yi na tsawon shekaru, ƙasar Sin ta riga ta gina tsarin…
Read More
Ya dace ƙasashen BRICS su yi ƙoƙarin tabbatar da tsaro da samar da cigaba ga duniya

Ya dace ƙasashen BRICS su yi ƙoƙarin tabbatar da tsaro da samar da cigaba ga duniya

Daga CMG HAUSA A wajen bikin ƙaddamar da ganawar ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS da aka yi ta kafar bidiyo da yammacin jiya Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi jawabi, inda ya jaddada wasu muhimman batutuwa biyu, dake haɗe da tsaro da ci gaba, ya kuma nanata cewa, a matsayinsu na ƙasashen dake bada gudummawa wajen gina duniya, ya kamata ƙasashen BRICS su tsaya haikan don fuskantar ƙalubaloli, da tabbatar da zaman karko, da samar da kuzari na raya hulɗoɗin ƙasa da ƙasa. Tsaron siyasa muhimmin jigo ne na hadin-gwiwar ƙasashen BRICS. Tuni shugaba Xi ya gabatar da…
Read More
Wang Wenbin: Fatanmu shi ne Amurka ta aiwatar da abubuwan da ta alƙawarta

Wang Wenbin: Fatanmu shi ne Amurka ta aiwatar da abubuwan da ta alƙawarta

Daga CMG HAUSA Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ƙasar sa na fatan Amurka za ta inganta kawancen ta da ƙasashen dake yankin Asiya da tekun Pacifik, za ta kuma ƙara azama wajen ingiza zaman lafiya da ci gaba, maimakon rura wutar rikici, da tada zaune tsaye a yankin. Wang ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na Juma’ar nan a birnin Beijing. A yau Juma’a ne shugaban Amurka Joe Biden ya isa Koriya ta Kudu, inda zai gana a karon farko da sabon shugaban ƙasar Yoon Suk-yeol. Kuma tun a ranar Laraba ne, mashawarcin…
Read More
An cimma nasarori wajen taron ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS

An cimma nasarori wajen taron ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS

Daga CMG HAUSA Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana a yau Jumma’a cewa, an cimma matsaya, da nasarori a wasu muhimman batutuwan da suka shafi tsaro da ci gaban duniya, a wajen taron ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS da aka yi ta kafar bidiyo a jiya Alhamis, matakin da ya share fage sosai a fannin siyasa, da gudanar da ganawar shugabannin ƙasashen BRICS karo na 14. Jiya Alhamis, memban majalisar gudanawar ƙasar Sin, wanda kuma shi ne ministan harkokin wajen ƙasar Wang Yi, ya jagoranci shawarwari ta kafar bidiyo, tsakanin ministocin harkokin waje…
Read More
Xi Jinping ya gabatar da jawabi ga taron ministocin wajen ƙasashe mambobin ƙungiyar BRICS

Xi Jinping ya gabatar da jawabi ga taron ministocin wajen ƙasashe mambobin ƙungiyar BRICS

Daga CMG HAUSA A yau Alhamis ne shugaban ƙasar Sin Xi jinping, ya gabatar da jawabi a yayin buɗe taron ministocin wajen ƙasashe mambobin ƙungiyar BRICS ta kafar bidiyo. Cikin jawabin na sa, Xi Jinping ya ce a halin yanzu, dalilan dake haifar da rashin kwanciyar hankali, da rashin tabbas, da rashin tsaro a harkokin ƙasa da ƙasa na ƙara bayyana. Amma duk da haka, jigon wannan zamanin da muke ciki na zaman lafiya, da neman ci gaba bai canza ba, kaza lika burin al’ummun duniya na samun kyakkyawar rayuwa bai sauya ba, haka kuma, fatan sassan ƙasa da ƙasa…
Read More
Baki biyu bai dace da matsayin Amurka ba

Baki biyu bai dace da matsayin Amurka ba

Daga CMG HAUSA Yayin da gwamnatocin ƙasashen Sin da Amurka ke ƙara azamar daidaita tsakani, da shawo kan sabani, da kaucewa mummunar takara, masharhanta na ganin mafi yawan matsalolin da ƙasashen 2 ke fuskanta na da nasaba ne da yadda Amurka ke karya ƙa’idoji, ko ra’ayoyin da sassan biyu suka amincewa. Daya daga muhimman batutuwa dake ci gaba da janyo hankalin duniya, don gane da takun sakar dake wakana tsakanin Sin da Amurka shi ne batun yankin Taiwan na ƙasar Sin, inda a wasu lokuta Amurka ta sha bayyana goyon bayan ta ga kasancewar yankin Taiwan ɓangare na ƙasar Sin…
Read More