Labarai

Cutar Korona: An samu ƙarin mutum 1,340 da suka harbu a faɗin ƙasa

Cutar Korona: An samu ƙarin mutum 1,340 da suka harbu a faɗin ƙasa

Daga FATUHU MUSTAPHA A halin da ake ciki, birnin tarayya, Abuja da jihar Legas da River da kuma Oyo, su ne jihohin da ke kan gaba wajen samun mafi yawan waɗanda suka harbu da cutar korona a tsakanin sa'o'i 24 da suka gabata. Bayanan Cibiyar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka ta Ƙasa (NCDC), sun nuna an samu ƙarin mutum 1,340 da suka kamu da cutar korona. Ƙarin da cibiyar ta ce ya shafi wasu jihohin ƙasar nan su 22, ciki har da Abuja 320, Lagos 275, Rivers 117, da kuma Oyo 100. Sauran sun haɗa da Sakkwato 3, Kaduna 31, Katsina 14,…
Read More
Yajin aiki: Muna nan kan bakanmu – SSANU/NASU

Yajin aiki: Muna nan kan bakanmu – SSANU/NASU

Daga AISHA ASAS Haɗaɗɗen Kwamitin Ƙungiyar Ma'aikatan Jami'o'i (NASU) da kuma Ƙungiyar Manyan Ma'aikatan Jami'o'i (SSANU), ya tsayar da ranar Juma'a (05/02/2021) a matsayin ranar da mambobin ƙungiyoyin biyu za su soma yajin aiki na sai baba-ta-gani sakamakon gazawar da suka ce gwamnati ta yi wajen biya musu buƙatunsu. Tun farko, sai da ƙungiyoyin suka bai wa gwamnati wa'adin makonni kan ta magance musu matsalolinsu ko kuma su tsunduma yajin aiki. Shugaban SSANU Muhammed Haruna, ya shaida wa Manhaja cewa, babu wata yarjejeniya da ƙungiyoyin suka cim ma da gwamnati kan janye ƙudirin shiga yajin aikin. Yana mai cewa, tattaunawar…
Read More
Fulani na da ‘yancin zama ko’ina a Nijeriya – Ƙungiyar Igbo

Fulani na da ‘yancin zama ko’ina a Nijeriya – Ƙungiyar Igbo

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Gamayyar Ma'aikata 'Yan Kudu Maso-gabas a Nijeriya da Ƙetare (CSEPNND), sun yi tir da ayyukan 'yan ƙungiyar IPOB ƙarƙashin jagorancin Nnamdi Kanu, musamman ma la'akari da yadda suke muzguna wa Fulani makiyaya a shiyarsu. A wata takardar bayani da shugaban ƙungiyar, Prof. Madumere Chika, ya fitar a ranar Alhamis wadda Jaridar Manhaja ta samu kwafinta, Chika ya ce Fulani makiyaya na da 'yancin zama ko'ina a faɗin Nijeriya ba tare da fuskantar muzgunawa ba kamar dai yadda Kundin Dokokin Ƙasa na 1999 ya nuna. Ƙungiyar ta cacciki Kanu da mabiyansa kan cewa sun sa ana yi…
Read More
NCDC ta samar da lambar tantance sahihancin bayanai

NCDC ta samar da lambar tantance sahihancin bayanai

Daga AISHA ASAS A matsayin wani mataki na sauƙaƙa wa 'yan Nijeriya iya tantance sahihancin bayanai game da cutar korona, Cibiyar Daƙile Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Ƙasa (NCDC) tare da taimakon Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), ta samar da lamba ta musamman da za ya taimaka wa 'yan ƙasa wajen tantance bayanai. NCDC ta ce, a duk lokacin da buƙatar neman tabbatar da sahihancin wani bayani ta taso, 'yan ƙasa na iya kiran lambar “6232” don tabbatar da ingancin wani bayani a kan korona da sauran cututtuka. A bayanin da Babban Daraktan NCDC, Dr Chikwe Ihekweazu, ya yi a Larabar…
Read More
Shirin kula da ilimin yara milyan 6.9 ya kankama – inji Gwamnatin Tarayya

Shirin kula da ilimin yara milyan 6.9 ya kankama – inji Gwamnatin Tarayya

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta sanar cewa, ta soma gudanar da shirinta na neman bai wa yaran da suka daina zuwa makaranta ilimi a faɗin ƙasa. Sanarwar hakan ta bayyana ne a shafin tuwita na Shugaban Ƙasa a Larabar da ta gabata. Idan dai za a iya tunawa, a Janairun da ya gabata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya kafa wani kwamiti na musamman mai mambobi 18 tare da ɗora masa nauyin kula da wannan shiri, ƙarƙashin jagorancin Ministar Jinƙai da Agaji da kuma Ministan Ilimi. Buhari ya ce, shirin zai maida hankali ne wajen karantar da yara darussan Lissafi…
Read More
Haɗin kan Neja da Kaduna abin yabo ne – El-Rufai

Haɗin kan Neja da Kaduna abin yabo ne – El-Rufai

Daga BASHIR ISAH Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya yaba wa takwaransa na jihar Neja, Abubakar Sani Bello, bisa haɗa kai da Kaduna wajen yaƙi da harkokin masu sace-sacen mutane a iyakokin Kaduna da Neja. El-Rufai ya yi wannan yabo ne yayin ziyarar da ya kai wa Gwamna Bello a Minna, babban birnin jihar. Babbar Sakatariyar Yaɗa Labarai ta gwamnan Neja, Mary Noel-Berje ta ce, El-Rufai ya yi ziyarar ne domin jajanta wa gwamnati da ma al'ummar jihar game da rashin wani fitaccen ɗan jihar da ya auku ba da daɗewa ba. Yayin ziyar, Gwamana El-Rufai ya ce, Neja…
Read More
Marigayi Momoh: “Dattijo mai dattako, mai kishin ƙasa, ɗan jarida abin koyi” – inji Tinubu

Marigayi Momoh: “Dattijo mai dattako, mai kishin ƙasa, ɗan jarida abin koyi” – inji Tinubu

Daga UMAR M. GOMBE Tsohon Gwamnan Jihar Legas kuma jigo a jam'iyyar APC mai mulki, Chief Bola Tinubu, ya bayyana marigayi Tony Momoh a matsayin "Dattijo mai dattako, mai kishin ƙasa kuma ɗan jarida abin koyi." A saƙon ta'aziyya da ya fitar ta hannun mai taimaka masa kan sha'anin labarai, Mr Tunde Rahman, Tinubu ya bayyana alhininsa dangane da mutuwar Tony Momoh. Yana mai cewa, "Na tuna wata tattaunawar da aka yi da shi da na karanta a ɗaya daga cikin jaridun ƙasar nan a 'yan kwanakin da suka gabata, inda ya bayyana irin son da yake yi wa ƙasarsa…
Read More
DSS ta yi gargaɗi kan take-taken neman tada rikici a ƙasa

DSS ta yi gargaɗi kan take-taken neman tada rikici a ƙasa

Daga AISHA ASAS Hukumar Tsaro ta DSS, ta yi gargaɗi kan take-taken da wasu mutane da kuma ƙungiyoyi ke yi na neman haddasa rikicin addini da na ƙabilanci a wasu sassan ƙasa. Jami'in Hulɗa da Jama'a na Ƙasa na hukumar, Dr Peter Afunanya, shi ne ya yi wannan gargaɗi a wani bayani da ya yi a Abuja, a ranar Laraba. Ko a ranar 11 ga Janairun da ya gabata, sai da hukumar ta yi makamancin wannan gargaɗi inda ta ce, akwai wasu da ke mummunan tanadi don tayar da rikicin addini a ƙasa. A cewar DSS, wuraren da ake hari…
Read More
Wata baƙuwar cuta ta fara kashe mutane a Sakkwato

Wata baƙuwar cuta ta fara kashe mutane a Sakkwato

Daga UMAR GWARANYO Gwamnatin Jihar Sokoto ta fidda wata sanarwa mai bayyana ɓarkewar wata sabuwar cuta a wani ɓangare na jihar. Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Gwamna Jihar, Aminu Waziri Tambuwal, ta bayyana cewa mutane huɗu sun mutu daga cutar. Haka kuma sanarwar ta nuna adadin mutanen da suke asibiti a halin yanzu suna karɓar magani sun haura 20. Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ya ce, “A yanzu haka mutane 24 na karɓar kulawa a asibitoci daban-daban a faɗin jihar. Amma an ƙirƙiri wani kwamiti da nufin bincikar cutar tare da gano maganin ta da rigakafin ta." Gwamnan ya ce…
Read More
Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Ƙungiyar Kare 'Yancin Zamantakewa Da Yaƙi Da Cin Hanci (SERAP), ta yi kira ga Shugaban Majalisar Dattawa Dr Ahmad Lawan, da takwaransa na Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Femi Gbajabiamila, a kan su buƙaci hukumomin yaƙi da rashawa su binciki badaƙalar ɓatan dabon da kasafin biliyan N4.4 na Majalisar Tarayya ya yi kamar yadda rahotannin binciken ofishin Babban Jami'in Bincike na Ƙasa suka nuna. A wata wasiƙa da ta samu sa hannun mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ƙungiyar ta ce, "Ta hanyar kwatanta jagoranci nagari a kan wannan batu, Majalisar Tarayya za ta iya nuna wa 'yan Nijeriya cewa ɓangaren yin…
Read More