17
Aug
Daga BASHIR ISAH Ya zuwa ranar Litinin ta makon gobe idan Allah Ya kai mu ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa da ya naɗa. Sanarwar da ta fito ta bakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ta ce bikin rantsarwa zai gudana ne a babban zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da misalin ƙarfe 10 na safe. Sanarwar ta ƙara da cewa 'yan rakiya biyu-biyu kacal aka amince wa ministocin su take musu baya zuwa wajen taron. “Ana sa ran ministocin kowanne ya zo da 'yan rikiya guda biyu. “Sannan…