Babban Labari

Kotun Faransa ta ƙwace jiragen Fadar Shugaban Nijeriya

Kotun Faransa ta ƙwace jiragen Fadar Shugaban Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumomi a Faransa da Switzerland sun kama wasu jiragen sama guda uku na Shugaban ƙasar Nijeriya. Kamen dai ya biyo bayan hukuncin da wata kotu a ƙasar Faransa ta yanke, inda ta bayar da izinin ƙwace jirgin saboda taƙaddamar kasuwanci da ta daɗe ta na yi tsakanin Jihar Ogun da wani kamfanin ƙasar China mai suna Zhongshan. Jiragen da suka haɗa da Dassault Falcon 7ɗ da ke filin tashi da saukar jiragen sama na Paris-Le Bourget da Boeing 737 da Airbus 330 da ke filin jirgin saman Basel-Mulhouse a ƙasar Switzerland an dakatar da…
Read More
Ambaliya: Uku sun rasu, 700 sun rasa matsuguni a Kebbi

Ambaliya: Uku sun rasu, 700 sun rasa matsuguni a Kebbi

Daga JAMIL GULMA, a Birnin Kebbi Wani ruwan sama da aka yi kama da bakin ƙwarya a waɗansu sassan Jihar Kebbi da aka soma tun ranar Juma'ar da ta gabata zuwa ranar Lahadi ya yi sanadiyyar rushewar gidaje sama da ɗari200, inda kimanin sama da mutane 700 suka rasa matsuguni, musamman a ƙananan hukumomin Argungu da Augie. Ruwan saman ya yi ƙamari a daren Lahadi, wanda ya sanya dole magidanta a ƙauyen Kamfani mai kimanin kilomita 10 daga Argungu kan hanyar Sakkwato kwasar kayansu zuwa filin Polo da ke kusa da ƙauyen. Malam Umar Muhammed Kamfani, wani magidanci, ya bayyana…
Read More
Yadda zanga-zangar matsin rayuwa ta ƙazance a Nijeriya

Yadda zanga-zangar matsin rayuwa ta ƙazance a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zanga-zangar nuna adawa da tsananin matsin rayuwa da ake ciki a Nijeriya wadda aka fara gudanarwa jiya Alhamis a duk faɗin ƙasar ta bar baya da ƙura a wasu jihohi, inda ake zargin wasu ɓata-gari da yin amfani da zanga-zangar wajen ɓata kayan gwamnati da fasa shagunan 'yan kasuwa ana sace kayan masarufi da wasu muhimman abubuwa da sauran ayyukan dabanci, lamarin da ya jefa al'umma cikin zulumi da takaici. Babban abin da matasan ke dogaro da shi game da kiraye-kirayen su na yin zanga-zangar shi ne matsin tattalin arziki. Al'ummar ƙasar na kokawa…
Read More
Albashi: Tinubu da NLC sun amince da ₦70,000

Albashi: Tinubu da NLC sun amince da ₦70,000

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da Naira 70,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata a Nijeriya. Ministan Labarai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya sanar da hakan jiya Alhamis yayin ganawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Ministan ya ce Shugaba Tinubu wanda ya sanar da hakan yayin taron da ya yi da shugabannin ƙungiyar ƙwadago, ya kuma ƙuduri aniyar bitar dokar albashi mafi ƙaranci duk bayan shekara uku. “Muna farin cikin sanar da ku a yau [Alhamis] cewa ƙungiyoyin ƙwadago da Gwamnatin Tarayya sun amince da ƙarin…
Read More
Za mu ɗauki mummunan mataki kan duk wanda aka kama da laifin maɗigo da luwaɗi-Gwamnatin Kano

Za mu ɗauki mummunan mataki kan duk wanda aka kama da laifin maɗigo da luwaɗi-Gwamnatin Kano

Daga Rabiu Sanusi Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya bai wa hukumar Hisbah umarnin daukar mataki kan wa su kungiyoyi da ake zargin da koyar da Luwaɗi da Maɗigo a Jihar Kano. Umarnin na Gwamnan na zuwa ne bayan zargin ɓullar wasu ƙungiyoyi dake fakewa da tallafawa makarantu suna yaɗa mummunar dabi’ar auren jinsi a jihar. Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Baba Halilu Dantiye ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar lahadin data gabata. Tun da farko dai kwamishinan ya ce gwamnatin jihar baza ta amince da auren jinsi ba…
Read More
Mutane 25 sun mutu, 53 sun jikkata a haɗarin mota a Kano – FRSC

Mutane 25 sun mutu, 53 sun jikkata a haɗarin mota a Kano – FRSC

Daga Ibrahim Hamisu, Kano Hukumar kiyaye haddura ta ƙasa FRSC reshen jihar Kano ta tabbatar da mutuwar matafiya 25, yayin da wasu 53 suka samu raunuka a wani hatsarin mota da ya afku a safiyar yau Litinin. Lamarin ya faru ne a kasuwar duniya ta Dangwairo da ke wajen birnin Kano. An ce matafiyan sun yo lodin su ne a cikin wata tirela wadda ita ma take dauke da shanu ta nufi Kudancin Nijeriya daga Maiduguri. Sai dai Tirelar ta yi karo da wata motar kuma ta yi ta'adi so sai inda mutane da dama suka mutu. Kwamandan hukumar FRSC…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙi Rarara

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙi Rarara

Daga Umar Garba a Katsina Wasu 'yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun afka gidan hajiya Halima Adamu, mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan Dauda Adamu Kahuru Rarara a gidanta dake Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja ta jihar Katsina. Rahotanni da Blueprint Manhaja ta samu na nuna cewar 'yan bindigar sun yi dirar mikiya a gidan hajiya Halima da misalin ƙarfe 1:30 na tsakar dare. Mazauna garin da lamarin ya faru a gabansu sun shaidawa jaridar Daily Trust cewa,  “A kafa suka zo, kuma kasancewar ba su yi harbi ba a lokacin da suka kai harin sun yi garkuwa da ita…
Read More
Tinubu ya rattaɓa hannu kan tsohon Taken Ƙasa ya zama doka

Tinubu ya rattaɓa hannu kan tsohon Taken Ƙasa ya zama doka

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanya ya rattaɓa hannu kan Dokar Taken Ƙasa inda a yanzu za a koma amfani da tsohon taken ƙasa wanda Turawan mulkin mallaka suka samar. Tuni dai wannan al'amari ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin 'yan ƙasa. Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya sanar da hakan yayin zaman da Majalusar ta yi a ranar Laraba. Haka nan, Akoabio ya ce Shugaba Tinubu ba zai yi wa Majalisar jawabi ba illa iyaka ya ƙaddamar da sabon taken na Nijeriya. Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya ce Tinubu ya soke gabatar da jawabin ne kasancewar Ranar…
Read More
Kotu ta ba wa ‘yan sandan Kano umarnin fitar da Aminu Ado daga Gidan Sarki na Nasarawa

Kotu ta ba wa ‘yan sandan Kano umarnin fitar da Aminu Ado daga Gidan Sarki na Nasarawa

Babbar Kotu a Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Alƙali Amina Adamu Aliyu, ta bai wa Kwamishinan 'Yan Sandan Kano umarni a kan su gaggauta fitar da Aminu Bayero daga Fadar Sarkin Nasarawa inda yake da zama a halin yanzu. Haka nan, Kotun ta ba da umarnin haramta wa Alhaji Aminu Ado Bayero da sauran sarakuna huɗun da aka tuɓe, ɗaukar kansu a matsayin sarakai har sai ta surari ƙarar da ke gabanta. Sauran da hanin ya shafa su ne tuɓaɓɓun sarakunan Bichi da Rano da Gaya da kuma Karaye. Wannan umarni ya biyo bayan ƙararar da lauyan mai ƙara, Ibrahim Isa…
Read More