Babban Labari

Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Daga BASHIR ISAH Ya zuwa ranar Litinin ta makon gobe idan Allah Ya kai mu ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa da ya naɗa. Sanarwar da ta fito ta bakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ta ce bikin rantsarwa zai gudana ne a babban zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da misalin ƙarfe 10 na safe. Sanarwar ta ƙara da cewa 'yan rakiya biyu-biyu kacal aka amince wa ministocin su take musu baya zuwa wajen taron. “Ana sa ran ministocin kowanne ya zo da 'yan rikiya guda biyu. “Sannan…
Read More
Gwamnati ta sake maka Emefiele a kotu kan zargin laifuffuka 20

Gwamnati ta sake maka Emefiele a kotu kan zargin laifuffuka 20

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta sake maka tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele a kotu inda take tuhumarsa da aikata laifuka 20. Wannan na zuwa ne bayan shigar da buƙatar janye ƙarar "mallakar bindiga ta haramtacciyar hanya" da gwamnatin ta shigar da fari kan Emefiele ɗin a Babban Kotun da ke zamanta a Legas. Daraktan sashen shigar da ƙararraki (DPP) a Ma'aikatar Shari'a ta Ƙasa, Mohammed Abubakar, ya sahaida wa alƙalin kotun, Nicholas Oweibo, cewar buƙatar janye ƙarar daga ɓangaren gwamnati ta taso ne domin ba da damar zurfafa bincike.…
Read More
Yaƙi na shirin ɓarkewa tsakanin ECOWAS da Nijar

Yaƙi na shirin ɓarkewa tsakanin ECOWAS da Nijar

*Ƙungiyar ECOWAS ta umarci dakarunta su yi shirin ko-ta-kwana*Tinubu ya aike da malaman Musulunci Nijar don shiga tsakani*Mu na bin Nijar bashin Naira Biliyan huɗu na lantarki, inji Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu matuƙar al’amura ba su sauya ba, yaƙi yana shirin varkewa tsakanin Ƙungiyar Tattalin Arziki ta Ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) ƙarƙashin jagorancin Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, da sojojin da suke riqe da madafun iko a Ƙasar Nijar bayan sun kifar da halastacciyar gwamnatin dimukraɗiyya a ƙarƙashin jagorancin Mohamed Bazoum, wanda sojojin suka hamɓarar. Hakan ya biyo bayan yadda shugabannin Ƙasashen ECOWAS…
Read More
Majalisa ta tabbatar da Malagi a matsayin Minista

Majalisa ta tabbatar da Malagi a matsayin Minista

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta tabbatar da mawallafin Jaridun Blueprint da Manhaja, Mohammed Idris Malagi daga Jihar Neja a matsayin Minista a Gwamnatin Bola Tinubu. Wannan na zuwa ne bayan shafi kimanin mako guda da Majalisar Dattawa ta yi tana tantance sunayen da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya aike mata don naɗa su muƙaman ministoci. Daga cikin waɗanda suka bi sawun Malagi wajen tabbatar da su a matsayin minista har da Dele Alake (Ekiti), tsohon Gwamnan Jihar Ribas Governor Nyesom Wike da tsohon minista a gwamnatin Muhammadu Buhari, Festus Keyamo, SAN, da sauransu. Malagi, Alake da Wike na daga…
Read More
NLC ta dakatar da ƙudirin tafiya yajin aiki – Fadar Shugaban Ƙasa

NLC ta dakatar da ƙudirin tafiya yajin aiki – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga BASHIR ISAH Fadar Shugaban Ƙasa ta ce Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) da ta 'yan Kasuwa (TUC) sun amice da su dakatar da ci gaba zanga-zangar da suka fara. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Mista Dele Alake, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar a Abuja. Ya ce an cim ma hakan ne biyo bayan tattauna da ƙungiyoyin suka yi da Shugaba Tinubu inda suka nuna gamsuwarsu dangane da tabbacin da Shugaban ya ba su na cim ma buƙatunsu. Yayin tattaunawar, Comrade Joe Ajaero ne ya jagoranci ɓangaren NLC, yayin da Comrade Festus Usifo ya…
Read More
Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi a yau

Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi a yau

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai yi wa 'yan ƙasa jawabi da misalin ƙarfi 07:00 na dare yau Litinin. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da ta fito ta bakin mai bai wa Tinubu shawara kan ayyuka na musamman da harkokin sadarwa, Dele Alake. Sanarwar ta ce ana buƙatar gidajen talabijin da rediyo da sauransu, da su jona da Tashar Talabijin ta Ƙasa da kuma Tashar Rediyo ta ƙasa don yaɗa jawabin Shugaba Ƙasar kai tsaye. Sai dai sanarwar ba ta fayyace dalilin da ya sa Tinubun zai yi 'yan ƙasa jawabin ba.
Read More
Tinubu ya naɗa Malagi, El-Rufai, Wike muƙamin minista

Tinubu ya naɗa Malagi, El-Rufai, Wike muƙamin minista

*An kasa samun matsaya kan ministocin Kano, Zamfara da Kebbi Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ƙarshe dai Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunayen mutane 28 da ya zaɓa a matsayin ministoci, domin naɗa su a matsayin mabobin Majalizar Zartarwar Tarayyar Nijeriya. Bayan an daɗe ana jiran jerin sunayen ne a jiya Alhamis Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya zo zauren majalisar da ƙarfe 12:05 na rana, inda bayan an yi addu’ar buɗe zaman zauren sai kuma ya bayyana cewa, majalisar za ta shiga wani zama na musamman. Bayan zaman ne ya fito ya bayyana jerin sunayen…
Read More
Sojoji sun kifar da gwamnatin Bazoum

Sojoji sun kifar da gwamnatin Bazoum

Daga BASHIR ISAH Sojoji a ƙasar Nijar sun yi wa Shugaban Ƙasar, Mohamed Bazoum, juyin mulki ranar Laraba da daddare sa'o'i bayan da masu tsaronsa suka tsare shi a fadarsa. A jawabin da ya yi wa 'yan ƙasa kai tsaye a tashar talabijin ta ƙasar, Colonel-Major Amadou Abdramane ya bayyana cewa, “sojoji da sauran hukumomin tsaro sun yanke shawarar jawo ƙarshen gwamnatin da kuka sani. “Wannan ya biyo bayan ci gaba da taɓarɓarewar tsaron ƙasar da kuma rashin walwala da ingancin tattalin arziki," in ji shi. Sojojin sun ce an rufe iyakokin ƙsar, sannan an kafa dokar hana zirga-zirga a…
Read More
Tinubu ya yi gargaɗi kan yunƙurin juyin mulki a Nijar

Tinubu ya yi gargaɗi kan yunƙurin juyin mulki a Nijar

Daga BASHIR ISAH Shugaban Nijeriya kuma Shugaban Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), Bola Ahmed Tinubu, ya yi gargaɗin cewa ECOWAS ba za ta yarda da duk wani al'amari da zai haifar da cikas ga zaɓaɓɓiyar gwamnati a yammacin Afirka ba. Tinubu ya yi wannan gargaɗi ne a matsayin martani kan fargabar yiwuwar juyin mulki a Jamhuriyar Nijar inda sojojin ƙasar suka tsare Shugaban Ƙasar, Mohamed Bazoum. Ya yi gargaɗin ne a matsayinsa na shugaban ECOWAS, cikin sanarwar da ya fitar a ranar Laraba, inda ya bayyana datse fadar shugaban ƙasar Nijar da sojojin suka yi a matsayin…
Read More
Yau take sabuwar shekarar Musulunci, 1445

Yau take sabuwar shekarar Musulunci, 1445

Daga BASHIR ISAH A wannan Larabar aka shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1445. A ranar Talata Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana Laraba, 19 ga Yulin 2023 a matsayin 1 ga watan Muharram na sabuwar shekarar ta 1445H. Kafin wannan lokaci, Basaraken ya buƙaci al’ummar Musulmi da su nemi jinjirin watan Muharram a ranar Litinin da ta gabata. Watan Muharram shi ne watan farko a kalandar Musulunci, kuma ɗaya daga cikin muhimman watannin da Musulunci yake bai wa fifiko. A wannan wata ne al’ummar Musulmin duniya kan yi azumin nafila a ranakun 9 da 10 ga…
Read More