Babban Labari

Tinubu ya tsuke wa ministocinsa bakin aljihu

Tinubu ya tsuke wa ministocinsa bakin aljihu

Ya umarci su su yi amfani da motoci uku a tawagarsu Ya bayyana haƙiƙanin dalilin korar wasu ministoci Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taƙaita yawan motocin da ministocinsa da sauran shugabannin hukumomin gwamnati ke amfani da su a tawagarsu zuwa guda uku, inda ya ce ba za a ƙara wa kowa ba. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin, Mista Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya ce, wannan wani mataki na daga cikin matakan da gwamnatinsa ke ɗauka ne na rage kashe kuɗaɗen gwamnati. Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu ya…
Read More
Yaushe Nijeriya za ta gyaru?

Yaushe Nijeriya za ta gyaru?

Gwamnatin Tinubu tana kan tafarki madaidaici, inji Bankin Duniya Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Idan aka yi la’akari da yanayin yadda Tarayyar Nijeriya ke tafiya, za a iya tunanin cewa, daga dukkan alamu babu ranar da ƙasar za ta samu irin cigaba ko ta gyaru kamar yadda akasarin talakawa suke tsammani da fatan samu, illa dai za a iya samun bunƙasa ta fuskar tafiyar zamani, wanda zamanin ne ya zo da shi da kansa, domin masu iya magana su na cewa, an daɗe a na ruwa ƙasa ta na shanyewa. Yanayin yadda ’yan siyasar ƙasar ke tafiyar gwamnatocinsu tun…
Read More
Tsohon alƙali ya gurfana bisa cin zarafin makauniya matar aure

Tsohon alƙali ya gurfana bisa cin zarafin makauniya matar aure

Masu buƙata ta musamman sun yi dafifi a kotun majistaren Zariya Daga MOH’D BELLO HABIB a Zariya An gurfanar da wani tsohon alƙali a gaban kotu bisa zargin cin zarafin wata makauniya matar aure a Jihar Kaduna, lamarin da ya hankalin al’umma, musamman masu buƙata ta musamman da suke yankin da abin ya faru. Wata kotun Majistare da ke Tudun Wada a Zariya ta Jihar Kaduna ta ɗage ci gaba da sauraron ƙarar wani tsohon alƙalin Babbar Kotun Shari'ar Musulunci, Mahmouda  Shehu, kan zargin cin zarafin wata matar aure makauniya mai suna Sa'adiyya Muhammed  a ranar 11 ga Nuwamba, 2024,…
Read More
Bikin ‘yancin kai: Jihar Kebbi ta ɗauki ɗumi

Bikin ‘yancin kai: Jihar Kebbi ta ɗauki ɗumi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  An kashe Shugaban Jam’iyyar APC a Jihar Kebbi: A bikin ‘yancin kan Nijeriya, rahotanni daga ƙaramar Hukumar mulki ta Suru da ke Jihar Kebbi sun bayyana cewa waɗansu da ba san ko su wane ne  ba ne sun afka gidan Shugaban Jam'iyyar APC na ƙaramar hukumar mulkin Alhaji Bala Bako Takalafiya inda suka yi awon gaba da shi da kuma ɗansa mai suna Hambali cikin daren Talatar da ta gabata. Wata majiya daga garin ɗakingari ta bayyana wa wakilinmu da cewa waɗansu mutane ɗauke da bindigogi ne suka shiga gidansa suka ɗauko shi tare da…
Read More
Shekaru 64 da ’yancin kai: Gyaran karaya Tinubu ke yi wa Nijeriya – Idris

Shekaru 64 da ’yancin kai: Gyaran karaya Tinubu ke yi wa Nijeriya – Idris

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce, Shugaba Tinubu na aiwatar da wasu tsare-tsare da sauye-sauye da aka tsara, domin magance kura-kuren da aka yi a baya, waɗanda suka karya tattalin arzikin ƙasar da kuma sanya Nijeriya kan turbar zama ƙasa mai ƙarfin tattalin arziki nan gaba kaɗan, inda hakan ba zai samu ba sai kowa ya yi sadaukarwa kuma an sha wahalar tare tamkar yadda gyarab karaya ya ke. Idris ya bayyana haka ne a cikin jawabinsa a Abuja ranar Alhamis a wani taron manema labarai, domin bayyana…
Read More
Yadda soja ya lahanta matasa biyu a Abuja

Yadda soja ya lahanta matasa biyu a Abuja

An sake shi bayan tsare shi Daga SADIYA SIDIYA a Abuja Ana zargin wani soja mai muƙamin ‘Last Chopra’ a Abuja mai suna Muhammed Ghanni Danladi da yi wa wasu ƙananan matasa guda biyu 'yan shekara 16, Sa’id Sidi Sa’id da Ibrahim Ali, wanda ake kira da Imam, dukan kawo wuƙan da ya haifar mu su da mummunan lahanin da ya jikkata su, inda har aka yi tsammanin sun ma rasa rayukansu. Lamarin ya faru ne a ranar Juma'a, 13 ga Satumba, 2024, a yankin Maraba cikin Ruga ’Yar Kasuwa da ke ƙaramar Hukumar Karu a Jihar Nasarawa kan iyakar…
Read More
Yadda ambaliyar Maiduguri ta girgiza al’ummar Nijeriya

Yadda ambaliyar Maiduguri ta girgiza al’ummar Nijeriya

Mutum 30 sun mutu, an ceto 719 Za a fuskanci ɓarkewar kwalara a Maiduguri, inji Majalisar ɗinkin Duniya Tinubu ya lashi takobin kawo ƙarshen ambaliya a Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ambaliyar ruwa da ta afku a Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno, da sanyin safiyar ranar Talata ta girgiza al'ummar Nijeriya, inda ta mamaye ɗaruruwan gidaje tare da lalata ɗimbin dukiya a jihar da uwa-uba asarar rayuka. Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta ƙasa NEMA ta tabbatar da cewa sama da mutane 200,000 ne suka rasa muhallansu. Hakazalika mutane 30 sun mutu a yayin da aka ceto wasu…
Read More
Ƙaranci da tsadar fetur: Mataimakin Shugaban ƙasa ya gana da Lokpobiri, Kyari da Ribadu don neman mafita

Ƙaranci da tsadar fetur: Mataimakin Shugaban ƙasa ya gana da Lokpobiri, Kyari da Ribadu don neman mafita

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya gayyaci ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur, Sanata Heineken Lokpobiri; da Babban Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin Mai na NNPC, Mele Kyari. Blueprint Manhaja ta kuma ruwaito cewa, an gayyaci Mai Bai Wa Shugaban ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, a jiya Alhamis a Fadar Shugaban ƙasa kan ƙarin farashin man fetur da kuma ƙarancinsa a Nijeriya. Shettima ya gana da mutanen ukun ne a ofishinsa na fadar Gwamnatin Tarayya Abuja. A ranar Talata ne kamfanin NNPC ya kara farashin man fetur daga N568 zuwa N855, N897 (ya…
Read More
Kisan Sarkin Gobir: Za a kai Gwamnan Sokoto Kotun Duniya

Kisan Sarkin Gobir: Za a kai Gwamnan Sokoto Kotun Duniya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Za a maka Gwamnan Jihar Sakkwato a Kotun Duniya akan kisan gillar da 'yan bindiga suka yi wa Mai Martaba Sarkin Gobir na Sabon Birni, Alhaji Isa Bawa, bayan garkuwa da shi da suka yi tsawon makonni uku. Shugaban gamayyar ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam na Afirka, Hon. Dr Sulaiman Sha'aibu Shinkafi, shi ne ya bayyana hakan cikin makon nan yayin da yake zantawa da manema labarai a Sakkwato. Dr Sulaiman Shuaibu ya ce gamayyar ƙungiyoyinsu 18 sun yi allawadai da kisan basaraken kana sun ɗauki laifin wannan ta'asa kacokan sun ɗora wa gwamnatin…
Read More
Ku kare kawunanku da kanku – Gwamnatin Katsina

Ku kare kawunanku da kanku – Gwamnatin Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dikko Umar Raɗɗa ta yi kira ga al'ummar jihar akan su tashi tsaye don su kare kansu daga hare-haren ɓarayin daji waɗanda ke ci gaba da addabar wasu ƙananan hukumonin jihar. Kwamishinan Tsaron Cikin Gida Na Jihar, Dakta Nasir Mu'azu ɗanmusa, ne ya yi wannan kira lokacin da yake ganawa da manema labarai a babban birnin jihar. Kwamishinan ya nuna damuwarsu game da yadda al'umma ke fargabar fito na fito da 'yan ta'addan duk da cewa sun fi 'yan bindigar yawan makamai. A cewar ɗanmusa, 'yan bindigar da ke…
Read More