Babban Labari

Zamfara: Dauda ya ƙara yi wa Matawalle fallasa

Zamfara: Dauda ya ƙara yi wa Matawalle fallasa

*Gwamna ya zargi ministan da wawure biliyoyin kuɗi na aikin filin jirgi*Za a gurfanar da masu hannu ciki a gaban kuliya Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga dukkan alamu zazzafar adawar siyasar dake tsakanin Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, da wanda ya gaje shi kuma Ƙaramin Ministan Tsaro, Muhammad Bello Matawalle, na ƙara yin tsamari a tsakaninsu, inda a baya-bayan nan gwamnan ya zargi ministan da wawure biliyoyin Dala na aikin gina filin jiragen sama na jihar ta Zamfara. Lawal ya ce, gwamnatin da ta shuɗe ta Bello Matawalle ta wawure biliyoyin Naira a filin jirgin sama na Zamfara, wanda daga…
Read More
Ana zargin almundahana a rabon kayan tallafin Kebbi 

Ana zargin almundahana a rabon kayan tallafin Kebbi 

*An dakatar da rabon tallafin Argungu Daga JAMIL GULMA a Kebbi  A ranar Juma'ar da ta gabata ne Gwamnan Jihar Kebbi, Malam Nasir Idris wanda shine Ƙauran Gwandu, ya ƙaddamar da rabon kayan tallafi a Ƙaramar Hukumar Maiyama, don rage raɗaɗin matsin tattalin arziki ga al'ummar jihar, inda kuma daga nan ya umarci kowacce ƙaramar hukumar mulki ta je ta raba a yankinta. Sai dai ba a nan gizo ke saƙa ba, saboda rabon kayan ya samu tarnaƙi yayin da a ke zargin tafka almundahana a waɗansu ƙananan hukumomi. Wata mata da ba ta so a bayyana sunanta ba ta…
Read More
Chicago: Zan dangana idan Kotun Ƙoli ta tsarkake Tinubu – Atiku

Chicago: Zan dangana idan Kotun Ƙoli ta tsarkake Tinubu – Atiku

*Ɗan takarar PDP ya ce ba don kansa yake wa Tinubu tone-tone ba*Siyasarka ta zo ƙarshe – APC ga Atiku*Ba na tsoro domin Buhari ya gama kassara kasuwancina a Nijeriya, inji Atiku Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ɗan takarar babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya yi iƙirarin cewa, idan har Kotun Ƙolin Nijeriya ta yanke hukuncin cewa, Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu tsarkakke ne shi, duk da satifiket ɗin da shi Atikun ya amso daga Jami’ar Chicago dake Birnin Ilinious, don ƙalubalantar sahihancin zaɓensa a 2023, to zai dangana ya haƙura…
Read More
Ranar Samun ‘Yancin Kan Ƙasa: Tinubu ya yi wa ma’aikata ƙarin albashi na wucin-gadi

Ranar Samun ‘Yancin Kan Ƙasa: Tinubu ya yi wa ma’aikata ƙarin albashi na wucin-gadi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana ƙarin albashi ga ma'aikatan gwamnati don rage musu raɗaɗin cire tallafin mai. Ya sanar da hakan ne a jawabinsa da ya yi wa 'yan ƙasa da safiyar Lahadi albarkacin Ranar Samun 'Yancin Kan Ƙasa, 1 ga Oktoba, 2023. Game da ƙarin, Tinubu ya ce ƙaramin ma'aikaci zai samu ƙarin N25,000 a albashinsa har na tsawon wata shida. Wannan na nufin ma'aikacin gwamnatin tarayya da ke karɓar albashi N30,000, yanzu N55,000 zai riƙa karɓa har na tsawon wata shida. Da alama dai ƙarin albashin na wucin gadi ne, kuma Shugaban bai yi ƙarin haske…
Read More
Ruɗani ya mamaye hukuncin kotun zaɓen Gwamnan Kaduna

Ruɗani ya mamaye hukuncin kotun zaɓen Gwamnan Kaduna

*Shugaban Kotun ya kori ƙarar*Alqalai biyu sun nemi yin tutsu?*Gwamna Sani ya yaba wa Ashiru Kudan*PDP ta kasa gamsuwa Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga dukkan alamu hukuncin da kotun sauraron ƙarar zaɓen kujerar Gwamnan Jihar Kaduna ta yanke ya jefa mutane da dama cikin ruɗani, inda da fari aka bayar da rahotannin da ke nuni da cewa, kotun ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba (wato inconclusive), to amma jim kaɗan bayan hakan sai kuma sababbin rahotanni suka nuna cewa, hukuncin yana magana ne akan tabbatar da Gwamna Uba Sani na Jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe…
Read More
Yau Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi

Yau Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi

Yau Lahadi ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai yi wa 'yan ƙasa jawabi bayan dawowa daga taron da ya halarta a Amurka. Taron shi ne karo na 78 da Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya wanda ya gudana a birnin New York. Bayan kammala taron ne Shugaba Tinubu ya ziyarci Paris da Faransa don taƙaitaccen hutu, in ji wata majiya. Tinubu ya iso gida ne sa'o'i kafin Ranar Samun 'Yancin Kan Nijeriya karo na 63, sannan kawana huɗu gabanin tsunduma yajin aikin da Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya da takwarorinta suka shirya. Da misalin ƙarfe 7:00am na wannan safiya…
Read More
An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

Jama'a sun shiga halin ruɗani game da shari'ar zaɓen gwamna a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne bayan da wani rahoto ya nuna Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe na Gwamnan Jihar ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba. Bayan kimanin awa guda da fitan rahoton, sai aka sake ganin wani rahoto na daban na cewa, kotun ta tabbatar da nasarar da Gwamna Uba Sani ya samu a zaɓen wanda hakan ke nuni da shi ne zaɓaɓɓen gwamnan jihar. Da yake yi wa Jaridar News Point Nigeria ƙarin haske game da hukuncin ta waya, lauyan Gwamna Sani, Ibrahim H O…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Kaduna, ta ayyana zaɓen gwamnan jihar da ya gudana ran 18 ga Maris a matsayin wanda bai kammala ba, wato 'inconclusive.' Kotun ta ayyana hakan ne a zaman yanke hukunci kan shari'ar da ta yi a ranar Alhamis. Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Victor Oviawe ta bai wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, da ta gudanar da zaɓen cike giɓi a cikin kwana 90. Da wannan hukuncin, ana sa ran INEC ta sake shirya zaɓe a gundumomi bakwai a tsakanin ƙananan hukumomi huɗu kuma a rumfunan zaɓe 24 masu ɗauke da masu kaɗa ƙuri'a…
Read More
Masu garkuwa sun ɗauki salon ɗauki-ɗaiɗai a Kebbi 

Masu garkuwa sun ɗauki salon ɗauki-ɗaiɗai a Kebbi 

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Masu garkuwa da mutane sun ɗauki sabon salo a waɗansu sassan Jihar Kebbi, inda yanzu a maimakon kai hari da suke yi a baya a cikin ayarin babura masu yawa, sun ɗauki salon ɗauki-ɗaiɗai, inda suke shiga cikin gari da tsakar dare su ɗauki mutum ɗaya ko biyu zuwa biyar maimakon ayarin mutane. Yankin ƙananan hukumomin Koko/Besse, Bagudo da Maiyama dai yanzu a nan ne waɗannan mutanen ke cin karensu ba babbaka duk da irin ƙoƙarin da hukumomin tsaro da ’yan sa-kai ke yi. A cikin daren ranar Larabar da ta gabata waɗannan mutanen sun…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamna a Kano, ta tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jam'iyyar NNPP sannan ta ayyana Yusuf Gawuna na Jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka guda a ranar 18 ga Maris. Bayan kammala zaɓe Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Yusuf Kabir a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Yayin da ɗan takarar APC, Nasir Gawuna, ya taya Kabir ɗin murnar lashe zaɓen ita kuwa jam'iyyarsa ta APC garzayawa kotu ta yi don ƙalubalantar sakamakon zaɓen. Yayin zaman yanke hukuncin da kotun ta yi a ranar Laraba, alƙalan kotun sun ba…
Read More